< Numbers 1 >

1 And the Lord spak to Moises in the deseert of Synay, in the tabernacle of the boond of pees, in the firste day of the secounde monethe, in the tother yeer of her goyng out of Egipt,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 and seide, Take ye `the summe of al the congregacioun of the sones of Israel, bi her kynredis, and howsis, and `the names of alle bi hem silf, what
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 euer thing is of male kynde fro the twentithe yeere and aboue, of alle the stronge men of Israel; and thou and Aaron schulen noumbre hem bi her cumpanies.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 And the princes of lynagis and of housis, in her kynredis, schulen be with you,
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 of whiche princes these ben the names; of Ruben, Elisur, the sone of Sedeur;
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 of Symeon, Salamyel, the sone of Suri Sadday;
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 of Juda, Naason, the sone of Amynadab; of Ysacar,
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Nathanael, the sone of Suar;
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 of Zabulon, Eliab, the sone of Elon; sotheli of the sones of Joseph,
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 of Effraym, Elisama, the sone of Amyud; of Manasses, Gamaliel the sone of Phadussur;
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 of Beniamyn, Abidan, the sone of Gedeon;
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 of Dan, Aiezer, the sone of Amysadday;
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 of Aser, Fegiel, the sone of Ochran;
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 of Gad, Elisaphan, the sone of Duel;
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 of Neptalym, Hayra, the sone of Henam.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These weren the noblest princes of the multitude, bi her lynagis, and kynredis, and the heedis of the oost of Israel,
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 whiche pryncis Moises and Aaron token, with al the multitude of the comyn puple.
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 And thei gaderiden in the firste dai of the secounde monethe, and telden hem bi kynredis, and housis, and meynees, and heedis, and names of alle by hem silf, fro the twentithe yeer and aboue,
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 as the Lord comaundide to Moises.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 And of Ruben the firste gendrid of Israel weren noumbrid, in the deseert of Synai, bi her generaciouns, and meynees, and housis, and bi the names of alle heedis, al thing that is of male kynde, fro `the twentithe yeer and aboue, of men goynge forth to batel,
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 sixe and fourti thousynd and fyue hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Of the sones of Symeon, bi her generaciouns, and meynees, and housis of her kyneredis, weren noumbrid, bi the names and heedis of alle, al that is of male kynde, fro `the twentithe yeer and aboue, of men goynge forth to batel,
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 nyn and fifty thousand and thre hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Of the sones of Gad, by generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro twenti yeer and aboue, alle men that yeden forth to batels,
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 fyue and fourti thousand sixe hundrid and fifti.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Of the sones of Juda, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, by the names of alle, fro `the twentithe yeer and aboue, alle men that miyten go to batels,
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 weren noumbrid foure and seuenti thousand and sixe hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Of the sones of Ysacar, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, bi the names of alle, fro `the twentithe yeer and aboue, alle men that yeden forth to batels,
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 weren noumbrid foure and fifti thousande and foure hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Of the sones of Zabulon, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro `the twentithe yeer and aboue, alle men that myyten go forth to batels,
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 seuene and fifti thousynde and foure hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Of the sones of Joseph, of the sones of Effraym, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro `the twentithe yeer and aboue, alle men that myyten go forth to batels,
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 fourti thousynde and fyue hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Forsothe of the sones of Manasses, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro the twentithe yeer and aboue, alle men that myyten go forth to batels,
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 two and thretti thousynd and two hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Of the sones of Beniamyn, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro twenti yeer and aboue, alle men that miyten go forth to batels,
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 fyue and thretti thousinde and foure hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Of the sones of Dan, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro `the twentithe yere and aboue, alle men that myyten go forth to batels,
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 two and sixti thousynde and seuene hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Of the sones of Aser, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro `the twentithe yeer and aboue, alle men that myyten go forth to batels,
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 fourti thousynde and a thousynde and fyue hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Of the sones of Neptalym, bi generaciouns, and meynees, and housis of her kynredis, weren noumbrid, bi the names of alle, fro `the twentithe yeer and aboue, alle men that myyten go forth to batels,
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 thre and fifty thousynde and foure hundrid.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 These men it ben, whiche Moises and Aaron and the twelue princes of Israel noumbriden, alle bi the housis `of her kynredis.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 And alle men of the sones of Israel bi her housis, and meynees, fro `the twentithe yeer and aboue, that myyten go forth to batels, weren togidere
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 sixe hundrid thousynde and thre thousynde of men, fyue hundred and fifti.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 Sotheli the dekenes in the lynage of her meynes weren not noumbrid with hem.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 And the Lord spak to Moises, and seide, `Nyle thou noumbre the lynage of Leuy,
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 nether sette thou the summe of hem with the sones of Israel;
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 but thou schalt ordeyne hem on the tabernacle of witnessing, and on alle the vessels therof, and what euer thing perteyneth to cerymonyes ether sacrifices. Thei schulen bere the tabernacle, and alle purtenaunces therof, and thei schulen be in seruyce, and schulen sette tentis bi the cumpas of the tabernacle.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 Whanne me schal go, the dekenes schulen do doun the tabernacle; whanne the tentis schulen be sette, thei schulen `reise the tabernacle. Who euer of straungeris neiyeth, he schal be slayn.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 Sotheli the sones of Israel schulen sette tentis, ech man bi cumpenyes, and gaderyngis, and his oost;
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 forsothe the dekenes schulen sette tentis bi the cumpas of the tabernacle, lest indignacioun be maad on the multitude of the sones of Israel; and thei schulen wake in the kepyngis of the `tabernacle of witnessyng.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Therfor the sones of Israel diden bi alle thingis whiche the Lord comaundide to Moises.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >