< Numbers 9 >
1 And the Lord spak to Moises, in the deseert of Synay, in the secounde yeer aftir that thei yeden out of the lond of Egipt, in the firste moneth,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
2 and seide, The sones of Israel make pask in his tyme,
“Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
3 in the fourtenthe day of this monethe, at the euentid, bi alle the cerymonyes and iustifiyngis therof.
A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
4 And Moises comaundide to the sones of Israel, that thei schulden make pask;
Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
5 whiche maden in his tyme, in the fourtenthe dai of the monethe, at euentid, in the hil of Synai; bi alle thingis whiche the Lord comaundide to Moises, the sones of Israel diden.
suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Lo! forsothe summen vncleene on the soule of man, that myyten not make pask in that dai, neiyiden to Moises and Aaron,
Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
7 and seiden to hem, We ben vncleene `on the soule of man; whi ben we defraudid, that we moun not offre an offryng to the Lord in his tyme, among the sones of Israel?
suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
8 To whiche Moises answeride, Stonde ye, that Y take counseil, what the Lord comaundith of you.
Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
9 And the Lord spak to Moises, and seide,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
10 Speke thou to the sones of Israel, A man of youre folk which is vncleene `on the soule, ether in the weie fer, make he pask to the Lord in the secounde monethe,
“Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
11 in the fourtenthe dai of the monethe, at euentid; with therf looues and letusis of the feeld he schal ete it.
Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
12 Thei schulen not leeue ony thing therof til the morewtid, and thei schulen not breke a boon therof; thei schulen kepe al the custom of pask.
Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
13 Forsothe if ony man is bothe cleene, and is not in the weie, and netheles made not pask, thilke man schal be distried fro hise puplis, for he offeride not sacrifice to the Lord in his tyme; he schal bere his synne.
Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
14 Also if a pilgrym and comelyng is anentis you, make he pask to the Lord, bi the cerymonyes and iustifiyngis therof; the same comaundement schal be anentis you, as wel to a comelyng as to a man borun in the loond.
“‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
15 Therfore in the dai in which the tabernacle was reisid, a cloude hilide it; sotheli as the licnesse of fier was on the tente fro euentid til the morewtid.
A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
16 Thus it was don continueli, a cloude hilide it bi dai, and as the licnesse of fier bi nyyt.
Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
17 And whanne the cloude that hilide the tabernacle was takun awei, thanne the sones of Israel yeden forth, and in the place where the cloude stood, there thei settiden tentis.
Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
18 At the comaundement of the Lord thei yeden forth, and at his comaundement thei settiden the tabernacle. In alle daies in whiche the cloude stood on the tabernacle, thei dwelliden in the same place.
Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
19 And if it bifelde that it dwellide in myche tyme on the tabernacle, the sones of Israel weren in the watchis of the Lord, and thei yeden not forth,
Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
20 in hou many euer daies the cloude was on the tabernacle. At the comaundement of the Lord thei reisiden tentis, and at his comaundement thei diden doun.
Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
21 If the cloude was fro euentid `til to the morewtid, and anoon in the morewtid hadde left, thei yeden forth; and if aftir a dai and nyyt it hadde go awei, thei scateriden, `ether diden doun, tentis.
Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
22 Whether in two monethis, ether in o monethe, ether in lengere tyme, `the cloude hadde be on the tabernacle, the sones of Israel dwelliden in the same place, and yeden not forth; but anoon as it hadde go awey, thei moueden tentis.
Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
23 Bi the word of the Lord thei settiden tentis, and bi his word thei wenten forth; and thei weren in the watchis of the Lord, bi his comaundement, bi the hond of Moyses.
Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.