< Numbers 31 >
1 And the Lord spak to Moyses, and seide,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Venge thou firste the sones of Israel of Madianytis, and so thou schalt be gaderid to thi puple.
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 And anoon Moises seide, Arme ye men of you to batel, that moun take of Madianytis the veniaunce of the Lord.
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4 Of ech lynage be chosun a thousynde men of Israel, that schulen be sent to batel.
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5 And of ech lynage thei yauen a thousynde, that is twelue thousynde of men, redi to batel;
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6 whiche Moises sente with Fynees, the sone of Eleazar, preest. And he bitook to hem hooli vesselis, and trumpis to make sown.
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
7 And whanne thei hadden fouyt ayens Madianytis, and hadden ouercome, thei killiden alle the malis,
Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
8 and `the kyngis of hem, Euy, and Reem, and Sur, and Hur, and Rebe, fyue princes of `the folc of hem. Also thei killiden bi swerd Balaam, the sone of Beor.
A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
9 And thei token the wymmen of hem, and the litle children, and alle beestis, and al purtenaunce of howshold; what euer thei myyten haue, thei spuyleden;
Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
10 flawme brente as wel citees, as litle townes and castels.
Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
11 And they token pray, and alle thingis whiche thei hadden take, as wel of men as of beestis, and thei brouyten to Moyses,
Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
12 and to Eleazar, preest, and to al the multitude of the sones of Israel. Forsothe thei baren othere `thingis perteynynge to vss, to the castels in the feldi places of Moab bisidis Jordan, ayens Jericho.
suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
13 Moises and Eleazar, preest, and alle the princes of the synagoge, yeden out in to the comyng of hem, with out the castels, `that is, of the tabernacle.
Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
14 And Moises was wrooth to the princes of the oost, to tribunes, and centuriouns, that camen fro batel;
Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
15 and he seide, Whi reserueden ye wymmen?
Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
16 whether it be not these that disseyueden the sones of Israel, at the suggestioun of Balaam, and maden you to do trespas ayens the Lord, on the synne of Phegor, wherfor also the puple was slayn?
Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
17 And therfor sle ye alle men, what euer thing is of male kynde, and litle children; and strangle ye the wymmen that knew men fleischli;
Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
18 forsothe reserue ye to you damesels, and alle wymmen virgyns,
amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
19 and dwelle ye with out the castels in seuene daies. He that sleeth a man, ether touchith a slayn man, schal be clensid in the thridde and the seuenthe dai;
“Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
20 and of al the pray, whether it is clooth, ether vessel, and ony thing maad redi in to thingis perteynynge to vss, of the skynnys and heeris of geet, and `of tre, it schal be clensid.
Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
21 And Eleazar, preest, spak thus to the men of the oost that fouyten, This is the comaundement of the lawe, which the Lord comaundide to Moises,
Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
22 The gold, and siluer, and bras, and yrun, and tiyn, and leed, and al thing that may passe by flawme, schal be purgid bi fier;
Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
23 sotheli what euer thing may not suffre fier, schal be halewid bi the watir of clensyng.
da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 And ye schulen waische youre clothis in the seuenthe dai, and ye schulen be clensid; and aftirward ye schulen entre in to the castels `of the tabernacle.
A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
25 And the Lord seide to Moises, Take ye the summe of tho thingis that ben takun, fro man `til to beeste,
Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
26 thou, and Eleazar, preest, and alle the princes of the comyn puple.
“Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
27 And thou schalt departe euenli the prey bytwixe hem that fouyten and yeden out to batel, and bitwixe al the multitude.
Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
28 And thou schalt departe a part to the Lord, of hem that fouyten, and weren in batel, `o soule of fiue hundrid, as wel of men, as of oxun, and of assis, and of scheep.
Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
29 And thou schalt yyue `that part to Eleazar, preest, for tho ben the firste fruytis of the Lord.
Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
30 Also of the myddil part of the sones of Israel, thou schalt take the fiftithe heed of men, and of oxun, and of assis, and of scheep, and of alle lyuynge beestis; and thou schalt yyue tho to the dekenes, that waken in the kepyngis of the tabernacle of the Lord.
Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
31 And Moyses and Eleazar diden, as the Lord comaundide.
Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
32 Forsothe the prey which the oost hadde take, was sixe hundrid fyue and seuenti thousynde of scheep,
Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
33 of oxun two and seuenti thousynde,
shanu 72,000
34 of assis sixti thousynde and a thousynde;
da jakuna 61,000.
35 the soules of persones of femal kynde, that knewen not fleischli men, two and thretti thousynde.
Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
36 And the myddil part was youun to hem that weren in the batel, of scheep thre hundrid seuene and thretti thousynde and fyue hundrid;
Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
37 of whiche sixe hundrid fyue and seuenti scheep weren noumbrid in to the part of the Lord;
tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
38 and of sixe and thretti thousynde oxun,
shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
39 two and seuenti oxun, and of thretti thousynde assis and fyue hundryd, oon and sixti assis;
jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
40 of sixtene thousynde persoones of men, twei and thretti persoones bifelden in to the `part of the Lord.
mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
41 And Moises bitook the noumbre of the firste fruytis of the Lord to Eleazar, preest, as it was comaundid to hym,
Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
42 of the myddil part of the sones of Israel, which he departide to hem that weren in batel.
Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
43 And of the myddil part that bifelde to the tother multitude, that is, of thre hundrid seuene and thretti thousynde scheep and fyue hundrid,
kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
44 and of sixe and thretti thousynde oxun,
shanu 36,000,
45 and of thretti thousynde assis and fyue hundrid, and of sixtene thousynde wymmen,
jakuna 30,500
46 Moyses took the fyftithe heed,
da mutane 16,000.
47 and yaf to the dekenes, that wakiden in the tabernacle of the Lord, as the Lord comaundide.
Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
48 And whanne the princes of the oost, and the tribunes and centuriouns hadden neiyed to Moises,
Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
49 thei seiden, We thi seruauntis han teld the noumbre of fiyters, whiche we hadden vndur oure hoond, and sotheli not oon failide;
suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
50 for which cause we offren `in the fre yiftis of the Lord, alle bi vs silf, that that we myyten fynde of gold in the pray, girdelis for `the myddil of wymmen, and bies of the armes, and ryngis, and ournementis of the arm nyy the hond, and bies of the neckis of wymmen, that thou preye the Lord for vs.
Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
51 And Moises and Eleazar, preest, token al the gold in dyuerse spices,
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
52 `ether kyndis, bi the weiyte of the seyntuarye, sixtene thousynde seuene hundrid and fifti siclis, of the tribunes, and centuriouns.
Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
53 For that that ech man rauyschide in the prey, was his owne;
Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
54 and thei baren the gold taken in to the tabernacle of witnessyng, in to the mynde of the sones of Israel, bifor the Lord.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.