< Numbers 23 >
1 And Balaam seide to Balaach, Bilde thou here to me seuene auteris, and make redi so many caluys, and rammes of the same noumbre.
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
2 And whanne he hadde do bi the word of Balaam, thei puttiden a calf and a ram to gidere on the auter.
Balak ya yi yadda Bala’am ya faɗa, sai su biyu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
3 And Balaam seide to Balaach, Stond thou a litil while bisidis thi brent sacrifice, while Y go, if in hap the Lord meete me; and Y schal `speke to thee what euer thing he schal comaunde.
Sa’an nan Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in koma wani wurin da yake a kaɗaice. Wataƙila Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Sai ya haura kan wani wurin da yake a kaɗaice a tudun.
4 And whanne he hadde go swiftli, God cam to hym; and Balaam spak to hym, and seide, Y reiside seuene auteris, and Y puttide a calf and a ram aboue.
Allah kuwa ya sadu da Bala’am. Bala’am ya ce, “Na shirya bagadai bakwai, na kuma miƙa bijimi guda da rago guda, a kan kowane bagade.”
5 Forsothe the Lord `puttide a word in his mouth, and seide, Turne ayen to Balaach, and thou schalt speke these thingis.
Ubangiji ya ba wa Bala’am saƙo ya ce, “Ka koma wurin Balak, ka faɗa masa wannan saƙo.”
6 He turnede ayen, and fond Balach stondynge bisidis his brent sacrifice, and alle the princes of Moabitis.
Saboda haka, sai Bala’am ya koma wurin Balak ya same shi tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dukan dattawan Mowab.
7 And whanne his parable `was takun, he seide, Balaach, the kyng of Moabitis, brouyte me fro Aran, fro the `hillis of the eest; and he seide, Come thou and curse Jacob; haaste thou, and greetli curse thou Israel.
Sai Bala’am ya furta abin da Allah ya faɗa masa ya ce, “Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab ya kawo ni daga gabashin duwatsu. Ya ce, ‘Zo, ka la’anta mini Yaƙub; zo, ka tsine Isra’ila.’
8 How schal Y curse whom God cursid not? bi what resoun schal Y `haue abhomynable whom God `hath not abhomynable?
Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?
9 Fro the hiyeste flyntis Y schal se hym, and fro litle hillis Y schal biholde hym; the puple schal dwelle aloone, and it schal not be arettid among hethene men.
Daga kan duwatsu na gan su, daga bisa kan tuddai na hange su. Na ga mutane da suke zaune su kaɗai ba sa ɗauki kansu ɗaya da al’ummai ba.
10 Who may noumbre the dust, that is, kynrede, of Jacob, and knowe the noumbre of the generacioun of Israel? My lijf die in the deeth of iust men, and my laste thingis be maad lijk hem!
Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yaƙub ko yă ƙidaya kashi ɗaya bisa huɗu na Isra’ila? Bari in mutu, mutuwar adali ƙarshena kuma yă zama kamar nasu!”
11 And Balaach seide to Balaam, What is this that thou doist? Y clepide thee, that thou schuldist curse myn enemyes, and ayenward thou blessist hem.
Balak ya ce wa Bala’am, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka, ka la’anta abokan gābana, sai ga shi albarka kake sa musu!”
12 To whom Balaam answeride, Whether Y may speke othir thing no but that that the Lord comaundith?
Bala’am ya ce, “Ba dole in faɗa abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”
13 Therfor Balaach seide to Balaam, Come with me in to anothir place, fro whennus thou se a part of Israel, and mayst not se al; fro thennus curse thou hym.
Sa’an nan Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su; a nan kana ganin sashe ne kawai, ba dukansu ba. Daga can kuwa, ka la’anta mini su.”
14 And whanne he hadde led Balaam in to an hiy place, on the cop of the hil of Phasga, he bildide seuene auteris to Balaam, and whanne calues and rammes weren put aboue,
Saboda haka ya ɗauke shi zuwa filin Zofim a ƙwanƙolin Fisga, a can ya gina bagadai bakwai, ya kuma miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
15 he seide to Balaach, Stonde here bisidis thi brent sacrifice, while Y go.
Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in je in sadu da Ubangiji a can.”
16 And whanne the Lord hadde `come to him, and hadde put `a word in his mouth, he seide, Turne ayen to Balach, and thou schalt seie these thingis to hym.
Ubangiji ya sadu da Bala’am, ya kuma ba shi saƙo ya ce, “Koma wurin Balak ka ba shi wannan saƙo.”
17 He turnyde ayen, and foond Balach stondynge bisidis his brent sacrifice, and the princis of Moabitis with hym. To whom Balach seide, What spak the Lord?
Saboda haka ya tafi ya same Balak tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dattawan Mowab. Balak ya tambaye Bala’am ya ce, “Mene ne Ubangiji ya ce?”
18 And whanne his parable `was takun, he seide, Stonde, Balach, and herkene; here, thou sone of Sephor. God is not `as a man,
Sai Bala’am ya furta saƙon da aka ba shi ya ce, “Tashi, Balak, ka saurara; ka kasa kunne gare ni, ɗan Ziffor.
19 that he lye, nethir he is as the sone of a man, that he be chaungid; therfor he seide, and schal he not do? he spak, and schal he not fulfille?
Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, shi ba ɗan mutum ba ne, da zai canja tunaninsa. Yana maganar abin da ba zai iya aikata ba ne? Yakan kuma yi alkawarin da ba zai iya cikawa ba?
20 Y am brouyt to blesse, Y may not forbede blessyng.
Na karɓi umarni in sa albarka; na kuwa sa albarka, ba zan iya janye ta ba.
21 Noon idol is in Jacob, nethir symylacre is seyn in Israel; his Lord God is with hym, and the sown of victorie of kyng is in hym.
“Bai ga mugunta a cikin Yaƙub ba, bai kuma ga wahala a Isra’ila ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su; sowar Sarki yana cikinsu.
22 The Lord God ledde hym out of Egipt, whos strengthe is lijk an vnicorn;
Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfi iri na kutunkun ɓauna.
23 fals tellyng bi chiteryng of bryddis, `ethir idolatrie, is not in Jacob, nethir fals dyuynyng is in Israel. In his tymes it schal be seide to Jacob and Israel, What the Lord hath wrought!
Ba wata maitar da za tă ci Yaƙub, ba sihiri da zai cuci Isra’ila. Yanzu za a ce game da Yaƙub da Isra’ila, ‘Duba abin da Allah ya yi!’
24 Lo! the puple schal rise to gidere as a lionesse, and schal be reisid as a lioun; the lioun schal not reste, til he deuoure prey, and drynke the blood of hem that ben slayn.
Mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfar zakanya; sun tā da kansu kamar zaki wanda ba ya hutawa sai ya cinye naman abin da ya kama ya kuma sha jinin abin da ya kama.”
25 And Balach seide to Balaam, Nether curse thou, nether blesse thou hym.
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka!”
26 And he seide, Whether Y seide not to thee, that what euer thing that God comaundide to me, Y wolde do this?
Bala’am amsa ya ce, “Ban faɗa maka zan yi kaɗai abin da Ubangiji ya ce ba?”
27 And Balach seide to hym, Come, and Y schal lede thee to an other place, if in hap it plesith God that fro thennus thou curse hym.
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Zo in kai ka wani wuri. Wataƙila zai gamshi Allah, yă bari ka la’anta mini su daga can.”
28 And whanne Balaach hadde led hym out on the `cop of the hil of Phegor, that biholdith the wildirnesse,
Balak kuwa ya ɗauki Bala’am zuwa ƙwanƙolin Feyor, wanda yake fuskantar hamada.
29 Balaam seide to hym, Bilde here seuene auteris to me, and make redi so many caluys, and rammes of the same noumbre.
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka kuma shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
30 Balaach dide as Balaam seide, and he puttide caluys and rammes, bi alle auteris.
Balak ya yi yadda Bala’am ya ce, ya kuwa miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.