< Numbers 10 >

1 And the Lord spak to Moises, and seide,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Make to thee twei siluerne trumpis betun out with hameris, bi whiche thou maist clepe togidere the multitude, whanne the tentis schulen be moued.
“Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
3 And whanne thou schalt sowne with trumpis, al the cumpeny schal be gaderid to thee at the dore of the tabernacle of the boond of pees.
Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
4 If thou schalt sowne onys, the princes and the heedis of the multitude of Israel schulen come to thee;
In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
5 but if a lengere and departid trumpyng schal sowne, thei that ben at the eest coost schulen moue tentis first.
Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
6 Forsothe in the secounde sown and lijk noise of the trumpe thei that dwellen at the south schulen reise tentis; and bi this maner othere men schulen do, whanne the trumpis schulen sowne in to goyng forth.
A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
7 Forsothe whanne the puple schal be gederid to gidere, symple cry of trumpis schal be, and tho schulen not sowne departyngli.
In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
8 The sones of Aaron preest schulen sowne with trumpis, and this schal be a lawful thing euerlastynge in youre generaciouns.
“’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
9 If ye schulen go out of youre lond to batel ayens enemyes that fiyten ayens you, ye schulen crye with trumpis sownynge, and the bithenkyng of you schal be bifor youre Lord God, that ye be delyuered fro the hondis of youre enemyes.
Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
10 If ony tyme ye schulen haue a feeste, and halidaies, and calendis, ye schulen synge in trumpis on brent sacrifices and pesible sacrifices, that tho be to you in to remembryng of youre God; Y am youre Lord God.
Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
11 In the secounde yeer, in the secounde monethe, in the twentithe dai of the monethe, the cloude was reisid fro the tabernacle of boond of pees.
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
12 And the sones of Israel yeden forth bi her cumpenyes fro deseert of Synay; and the cloude restide in the wildirnesse of Faran.
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
13 And the sones of Juda bi her cumpenyes, of whiche the prince was Naason, the sone of Amynadab, moueden first tentis,
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
14 bi the Lordis comaundement maad in the hond of Moises.
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15 In the lynage of the sones of Ysacar the prince was Nathanael, the sone of Suar.
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16 In the lynage of Sabulon the prince was Heliab, the sone of Helon.
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
17 And the tabernacle was takun doun, which the sones of Gerson and of Merary baren, and `yeden out.
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
18 And the sones of Ruben yeden forth bi her cumpenyes and ordre, of whiche the prince was Helisur, the sone of Sedeur.
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
19 Forsothe in the lynage of the sones of Symeon the prince was Salamyel, the sone of Surisaddai.
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
20 Sotheli in the lynage of Gad the prince was Helisaphath, the sone of Duel.
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
21 And the sones of Caath yeden forth, and baren the seyntuarie; so longe the tabernacle was borun, til thei camen to the place of reisyng therof.
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
22 Also the sones of Effraym, bi her cumpanyes, moueden tentis, in whos oost the prince was Elisama, the sone of Amyud.
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
23 Forsothe in the lynage of the sones of Manasses the prince was Gamaliel, the sone of Phadussur.
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
24 And in the lynage of Beniamyn the duk was Abidan, the sone of Gedeon.
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
25 The sones of Dan, bi her cumpenyes, yeden forth the laste of alle tentis, in whos oost the prince was Aizer, the sone of Amysaddai.
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
26 Sotheli in the lynage of the sones of Aser the prince was Phegiel, the sone of Ochran.
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
27 And in the lynage of the sones of Neptalym the prince was Haira, the sone of Henan.
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
28 These ben the castels and the goinges forth of the sones of Israel, bi her cumpenyes, whanne thei yeden out.
Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
29 And Moises seide to Heliab, the sone of Raguel, of Madian, his alie `ethir fadir of his wijf, We goon forth to the place which the Lord schal yyue to vs; come thou with vs, that we do wel to thee, for the Lord bihiyte goode thingis to Israel.
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
30 To whom he answeride, Y schal not go with thee, but Y schal turne ayen in to my lond, in which Y was borun.
Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
31 And Moises seide, Nyle thou forsake vs, for thou knowist in whiche places we owen to sette tentis, and thou schalt be oure ledere;
Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
32 and whanne thou schalt come with vs, what euer thing schal be the beste of the richessis whiche the Lord schal yyue to vs, we schulen yyue to thee.
In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
33 And therfor thei yeden forth fro the hil of the Lord the weie of thre daies; and the arke of boond of pees of the Lord yede bifor hem, bi thre daies, and purueyde the place of tentis.
Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
34 And the cloude of the Lord was on hem bi day, whanne thei yeden.
A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 And whanne the arke was reisid, Moises seide, Ryse thou, Lord, and thin enemyes be scaterid, and thei that haten thee, fle fro thi face;
Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
36 forsothe whanne the arke was put doun, he seide, Lord, turne ayen to the multitude of the oost of Israel.
Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”

< Numbers 10 >