< Nehemiah 9 >
1 Forsothe in the foure and twentithe dai of this monethe, the sones of Israel camen togidere in fastyng,
A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, Isra’ilawa suka taru, suna yin azumi, suna sa rigunan makoki, suna kuma zuba toka a kansu.
2 and in sackis, and `erthe was on hem. And the seed of the sones of Israel was departid fro ech alien sone. And thei stoden bifor the Lord, and knoulechiden her synnes, and the wickidnessis of her fadris.
Waɗanda suke zuriyar Isra’ilawa suka ware kansu daga dukan baƙi. Suka tsaya, suka kuma furta zunubansu da muguntar kakanninsu.
3 And thei risiden togidere to stonde; and thei redden in the book of the lawe of `her Lord God fouresithis in the dai, and fouresithis in the niyt; thei knoulechiden, and herieden `her Lord God.
Sa’ad da suke nan a tsaye, aka ɗauki awa uku ana karanta Littafin Dokar Ubangiji Allahnsu. Aka kuma ɗauki awa uku ana sujada ga Ubangiji Allahnsu.
4 Forsothe `thei risiden on the degree, of dekenes, Jesuy, and Bany, Cedynyel, Remmy, Abany, Sarabie, Bany, and Chanany.
A kan dakalin kuwa akwai Lawiyawa, wato, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani da Kenani tsaye, waɗanda suka kira da babbar murya ga Ubangiji Allahnsu.
5 And the dekenes crieden with grete vois to her Lord God. And Jesue, and Cedyniel, Bonny, Assebie, Serebie, Arabie, Odaie, Sebua, and Facaia, seiden, Rise ye, and blesse ye `youre Lord God fro without bigynnyng and til in to with outen ende; and blesse thei the hiye name of thi glorie in al blessyng and preysyng.
Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.
6 And Esdras seide, Thou thi silf, Lord, art aloone; thou madist heuene and the heuene of heuenes, and al the oost of tho heuenes; thou madist the erthe and alle thingis that ben there ynne; `thou madist the sees and alle thingis that ben in tho; and thou quikenyst alle these thingis; and the oost of heuene worschipith thee.
Kai kaɗai ne Ubangiji. Kai ka yi sammai, har ma da sama sammai, da dukan rundunar taurari, da duniya da kuma dukan abin da yake cikinta, da tekuna da dukan abubuwan da suke cikinsu. Ka ba da rai ga kome, kuma rundunonin sama suna maka sujada.
7 Thou thi silf art the Lord God, that chesidist Abram, and leddist hym out of the fier of Caldeis, and settidist his name Abraham;
“Kai ne Ubangiji Allah, wanda ya zaɓi Abram, ya fitar da shi daga Ur na Kaldiyawa, ya kuma ba shi suna Ibrahim.
8 and foundist his herte feithful bifor thee, and thou hast smyte with hym a boond of pees, that thou woldist yyue to hym the lond of Cananei, of Ethei, of Euey, and of Ammorrei, and of Pherezei, and of Jebuzei, and of Gergesei, that thou woldist yyue it to his seed; and thou hast fillid thi wordis, for thou art iust.
Kai ka sami zuciyarsa da aminci a gare ka, ka kuma yi alkawari da shi cewa za ka ba zuriyarsa ƙasar Kan’aniyawa, da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, da ta Yebusiyawa, da kuma ta Girgashiyawa. Ka kiyaye alkawarinka domin kai mai adalci ne.
9 And thou hast seyn the turment of oure fadris in Egipt, and thou herdist the cry of hem on the reed see.
“Ka ga wahalar kakanninmu a Masar; ka kuwa ji kukansu a Jan Teku.
10 And thou hast youe signes and grete wondris in Farao, and in alle hise seruauntis, and in al the puple of that lond; for thou knowist, that thei diden proudli ayens oure fadris; and thou madist to thee a name, as also in this dai.
Ka aika da alamu masu banmamaki da al’ajabai a kan Fir’auna, a kan dukan shugabanninsa da kuma a kan dukan mutanen ƙasarsa, gama ka ga irin danniyar da suka yi wa mutanenka. Ka samo wa kanka suna, wadda ta dawwama har yă zuwa yau.
11 And thou departidist the see bifor hem, and thei passiden thorou the `myddis of the see in the drie place; forsothe thou castidist doun the pursueris of hem into depthe, as a stoon in strong watris.
Ka raba teku a gaban kakanninmu, saboda su wuce cikinsa a busasshiyar ƙasa, amma ka hallaka masu binsu cikin zurfafa, nutse kamar dutse a cikin ruwa.
12 And in a piler of cloude thou were the ledere of hem bi dai, and in a piler of fier bi nyyt, that the weie, bi which thei entriden, schulde appere to hem.
Da rana ka bishe kakanninmu da girgije, da dare kuwa ka bishe su da ginshiƙin wuta don ka ba su haske a hanyar da za su bi.
13 Also thou camest doun at the hil of Synai, and spakist with hem fro heuene, and thou yauest to hem riytful domes, and the lawe of trewthe, cerymonyes, and goode comaundementis.
“Ka sauko a kan Dutsen Sinai; ka yi musu magana daga sama. Ka ba su ƙa’idodi da dokokin da suke masu adalci da kuma daidai, ka ba su farillai da umarnai da suke da kyau.
14 And thou schewidist to hem an halewid sabat; and thou comaundidist `to hem comaundementis, and cerymonyes, and lawe, in the hond of Moises, thi seruaunt.
Ka sanar da su Asabbacinka mai tsarki, ka kuma ba su umarnai, da farillai, da kuma dokoki ta wurin bawanka Musa.
15 Also thou yauest to hem breed fro heuene in her hungur; and thou leddist out of the stoon watir to hem thirstinge; and thou seidist to hem, that thei schulden entre, and haue in possessioun the lond, on which lond thou reisidist thin hond, that thou schuldist yyue it to hem.
Cikin yunwansu ka ba su burodi daga sama, cikin ƙishirwansu kuma ka fitar musu ruwa daga dutse. Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka rantse ta wurin ɗaga hannu cewa za ka ba su.
16 But `thei and oure fadris diden proudli, and maden hard her nollis, and herden not thi comaundementis.
“Amma su kakanninmu, suka yi fariya da taurinkai, ba su kuwa yi biyayya ga umarnanka ba.
17 And thei nolden here; and thei hadden not mynde of thi merueils, which thou haddist do to hem; and thei maden hard her nollis; and thei yauen the heed, that thei `weren al turned to her seruage as bi strijf; but thou art God helpful, meke, and merciful, abidynge longe, `ether pacient, and of myche merciful doyng, and forsokist not hem;
Suka ƙi su saurare ka, suka kāsa tuna da mu’ujizan da ka aikata a cikinsu. Suka yi taurinkai, cikin tawayensu kuma suka naɗa shugaba don su koma bautarsu. Amma kai Allah ne mai gafartawa, mai alheri da jinƙai, mai jinkirin fushi, mai yalwar ƙauna. Saboda haka ba ka yashe su ba,
18 and sotheli whanne thei hadden maad to hem a yotun calf, as bi strijf, and hadden seid, This is thi God, that `ledde thee out of Egipt, and thei diden grete blasfemyes.
ko ma sa’ad da suka yi wa kansu siffar ɗan maraƙi, suka ce, ‘Wannan shi ne allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar,’ ko sa’ad da suka yi saɓo mai bantsoro.
19 But thou in thi many mercyes leftist not hem in deseert; for a piler of cloude yede not awei fro hem bi the dai, that it schulde lede hem in to the weie; and a piler of fier yede not awei `fro hem bi nyyt, that it schulde schewe to hem the weie, bi which thei schulden entre.
“Saboda jinƙanka mai girma, ba ka yashe su a hamada ba. Da rana, ginshiƙin girgije bai daina bishe su a hanyarsu ba, da dare kuma ginshiƙin wuta bai daina haskakawa a hanyar da za su bi ba.
20 And thou yauest to hem thi good Spirit, that tauyte hem; and thou forbedist not thin aungels mete fro her mouth, and thou yauest to hem water in thirst.
Ka ba da Ruhunka mai kyau don yă koyar da su. Ba ka janye Manna naka daga bakunansu ba, ka kuma ba su ruwa don ƙishirwansu.
21 Fourti yeer thou feddist hem in deseert, and no thing failide to hem; her clothis wexiden not elde, and her feet weren not hirt.
Shekaru arba’in ka riƙe su a cikin hamada; ba su rasa kome ba, rigunansu ba su yage ba, ƙafafunsu kuwa ba su kumbura ba.
22 And thou yauest to hem rewmes, and puplis; and thou departidist lottis, `ether eritagis, to hem, and thei hadden in possessioun the lond of Seon, and the lond of the kyng of Esebon, and the lond of Og, kyng of Basan.
“Ka ba su mulkoki da al’ummai, kana ba su har ma da ƙasashen da suke jeji. Suka ci ƙasar Sihon na sarkin Heshbon da ƙasar Og inda sarkin Bashan yake mulki.
23 And thou multipliedist the sones of hem, as the sterris of heuene; and thou brouytist hem to the lond, of which thou seidist to her fadris, that thei schulden entre, and holde it in possessioun.
Ka sa’ya’yansu maza suka yi yawa kamar taurarin sararin sama, ka kuma kawo su cikin ƙasar da ka faɗa wa kakanninsu su shiga su mallake.
24 And the sones of Israel camen, and hadden the lond in possessioun; and bifor hem thou madist low the dwellers of the lond, Cananeis; and thou yauest hem in to the hondis of the sones of Israel, and the kyngis of hem, and the puplis of the lond, that thei diden to hem, as it pleside hem.
’Ya’yansu maza suka shiga suka kuma mallaki ƙasar. A gabansu ka rinjayi Kan’aniyawan da suke zama a cikin ƙasar; ka ba da Kan’aniyawa a gare su, tare da sarakunansu da kuma mutanen ƙasar, su yi da su yadda suke so.
25 And thei token citees maad strong, and fat erthe; and thei hadden in possessioun housis fulle of alle goodis, cisternes maad of othere men, vineris, and places of olyues, and many apple trees. And thei eeten, and weren fillid, and weren maad fat; and hadden plentee of ritchessis `in thi greet goodnesse.
Suka kame birane masu katanga masu ƙarfi, da ƙasa masu ba da amfani; suka mallaki gidaje cike da kowane irin abu mai kyau, da rijiyoyin da aka riga aka haƙa, da gonakin inabi, da gonakin itatuwan zaitun da kuma itatuwan ba da’ya’ya a yalwace a ciki. Suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba; suka ji daɗi cikin alherinka mai girma.
26 Sotheli thei terriden thee to wrathfulnesse, and yeden awei fro thee, and castiden awei thi lawe bihynde her backis; and thei killiden thi prophetis, that witnessiden to hem, that thei schulden turne ayen to thee; and thei diden grete blasfemyes.
“Amma suka yi rashin biyayya suka kuma yi tawaye gare ka; suka sa dokarka a bayansu. Suka kashe annabawanka waɗanda suka gargaɗe su don su mai da su gare ka; suka aikata saɓo mai bantsoro.
27 And thou yauest hem in to the hond of her enemyes; and thei turmentiden hem; and in the tyme of her tribulacioun thei crieden to thee; and thou herdist them fro heuyn, and bi thi many merciful doyngis thou yauest hem sauyours, that sauyden hem fro the hond of her enemyes.
Saboda haka ka miƙa su ga abokan gābansu waɗanda suka yi musu danniya. Amma sa’ad da ake danniyarsu sai suka yi kuka gare ka. Daga sama ka ji su, cikin jinƙanka mai girma kuwa ka ba su mai ceto, wanda ya fisshe su daga hannun abokan gābansu.
28 And whanne thei hadden restid, thei turneden ayen to do yuel in thi siyt; and thou forsokist hem in the hond of her enemyes, and enemyes hadden hem in possessioun; and thei weren conuertid, and thei crieden to thee; forsothe thou herdist hem fro heuene, and delyueridist hem `in thi mercies in many tymes.
“Amma nan da nan, da suka sami hutu, sai suka sāke aikata abin da yake mugu a idonka. Sai ka yashe su ga hannun abokan gābansu don su yi mulki a kansu. Sa’ad da suka yi kuka kuma gare ka, ka ji daga sama, cikin jinƙanka kuma ka fisshe su sau da sau.
29 And thou witnessidist to hem, that thei schulden turne ayen to thi lawe; but thei diden proudli, and herden not thin heestis, and synneden in thi domes, whiche a man that schal do schal lyue in tho; and thei yauen the schuldre goynge awei, and thei maden hard her nol.
“Ka gargaɗe su su dawo ga dokarka, amma suka yi fariya, suka bijire wa umarnanka. Suka yi zunubi game da farillanka waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu in ya yi biyayya da su. Cikin taurinkai suka juye bayansu daga gare ka, suka zama masu taurinkai, suka kuma ƙi su saurara.
30 And thou drowist along many yeeris on hem, and thou witnessidist to hem in thi Spirit bi the hond of thi prophetis; and thei herden not; and thou yauest hem in to the hond of the puplis of londis.
Shekaru masu yawa ka yi haƙuri da su. Ta wurin Ruhunka ka gargaɗe su ta wurin annabawa. Duk da haka ba su kasa kunne ba, saboda haka ka miƙa su ga maƙwabtansu.
31 But in thi mercies ful manye thou madist not hem in to wastyng, nethir thou forsokist hem; for thou art God of merciful doynges, and meke.
Amma cikin tausayinka mai girma ba ka kawo su ga ƙarshe ko ka yashe su ba, gama kai Allah ne mai alheri da kuma mai jinƙai.
32 Now therfor, oure Lord God, greet God, strong, and ferdful, kepynge couenaunt and merci, turne thou not awei thi face in al the trauel that foond vs, oure kyngis, and oure princes, and oure fadris, and oure preestis, and oure profetis, and al thi puple, fro the daies of kyng Assur til to this dai.
“To yanzu, ya Allahnmu, mai girma, mai iko, da kuma mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna, kada ka bar dukan wannan wahala ta zama kamar marar muhimmanci a idanunka, wahalar da ta zo a kanmu, a kan sarakunanmu da shugabanni, a kan firistocinmu da annabawa, a kan kakanninmu da kuma dukan mutanenka, daga kwanakin sarakunan Assuriya har yă zuwa yau.
33 And thou art iust in alle thingis, that camen on vs, for thou didist trewthe to vs; but we han do wickidli.
Cikin dukan abubuwan da suka faru da mu, ka kasance mai adalci; ka yi aminci, yayinda mu kuwa muka aikata mugu.
34 Oure kyngis, and oure princes, oure prestis, and fadris `diden not thi lawe; and thei perseyueden not thin heestis and witnessyngis, whiche thou witnessidist in hem.
Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu da kuma kakanninmu ba su bi dokarka ba, ba su ma mai da hankali ga umarnanka ko gargaɗin da ka yi musu ba.
35 And thei in her good rewmes, and in thi myche goodnesse, which thou yauest to hem, and in the largest lond and fat, whych thou haddist youe in the siyt of hem, serueden not thee, nether turneden ayen fro her werste studies.
Ko ma yayinda suke a masarautarsu, suna jin daɗin girmar kyautatawarka gare su, cikin ƙasar mai girma, da kuma mai fāɗin da ka ba su, ba su bauta maka ko su juye daga mugayen hanyoyinsu ba.
36 Lo! we `vs silf ben thrallis to dai; and the lond which thou yauest to oure fadris, that thei schulden ete the breed therof, and the goodis that ben therof, `is thral; and we `vs silf ben thrallis, `ethir boonde men, in that lond.
“Amma duba, mu bayi ne a yau, bayi a ƙasar da ka ba kakanninmu don su ci amfaninta da kuma waɗansu abubuwa masu kyau da take bayarwa.
37 And the fruytis therof ben multiplied to kyngis, whiche thou hast set on vs for oure synnes; and thei ben lordis of oure bodies, and of oure beestis, bi her wille, and we ben in greet tribulacioun.
Saboda zunubanmu, yalwar girbin da muke samu yana tafiya wurin sarakunan da ka sa a kanmu. Suna mulki bisa jikunanmu, da bisa garkenmu yadda suka ga dama. Muna cikin baƙin ciki.
38 Therfor on alle these thingis we `vs silf smyten and writen boond of pees, and oure princes, oure dekenes, and oure prestis aseelen.
“Saboda wannan duka, muna yin zaunannen alkawari, muna sa shi a rubuce, shugabanninmu kuwa da Lawiyawanmu, da firistocinmu suna buga hatimansu a kai.”