< Nehemiah 5 >

1 And greet cry of the puple and of her wyues was maad ayens her britheren Jewis.
To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
2 And there weren that seiden, Oure sones and oure douytris ben ful manye; take we wheete for the prijs of hem, and ete we, and lyue.
Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
3 And there weren that seiden, Sette we forth oure feeldis, and vyneris, and oure howsis, and take we wheete in hungur.
Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
4 And othere men seiden, Take we money bi borewyng in to the tributis of the kyng, and yyue oure feeldis and vyneris.
Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
5 And now as the fleischis of oure britheren ben, so and oure fleischis ben; and as ben the sones of hem, so and oure sones ben; lo! we han maad suget oure sones and oure douytris in to seruage, and seruauntissis ben of oure douytris, and we han not wherof thei moun be ayenbouyt; and othere men han in possessioun oure feeldis, and oure vyneris.
Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
6 And Y was ful wrooth, whanne Y hadde herde the cry of hem bi these wordis.
Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
7 And myn herte thouyte with me, and Y blamede the principal men and magistratis; and Y seide to hem, Axe ye not vsuris, `ech man of youre britheren. And Y gaderide togidire a greet cumpeny ayens hem,
Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
8 and Y seide to hem, As ye witen, we bi oure power ayenbouyten oure britheren Jewis, that weren seeld to hethene men; and ye therfor sillen youre britheren, and schulen we ayenbie hem? And thei holden silence, and founden not what thei schulen answere.
Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
9 And Y seide to hem, It is not good thing, which ye doon; whi goen ye not in the drede of oure God, and repreef be not seid to vs of hethene men, oure enemyes?
Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
10 Bothe Y and my britheren, and my children, han lent to ful many men monei and wheete; in comyn axe we not this ayen; foryyue we alien money, which is due to vs.
Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
11 Yelde ye to hem to dai her feeldis, and her vyneris, her olyue places, and her housis; but rather yyue ye for hem bothe the hundrid part `of money of wheete, of wyn, and of oile, which we weren wont to take of hem.
Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
12 And thei seiden, We schulen yelde, and we schulen axe no thing of hem; and we schulen do so as thou spekist. And Y clepide the preestis, and Y made hem to swere, that thei schulden do aftir that, that Y hadde seid.
Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
13 Ferthermore Y schook my bosum, and Y seide, So God schake awei ech man, `that fillith not this word fro his hows, and hise trauels; and be he schakun awei, and be he maad voide. And al the multitude seide, Amen; and thei herieden God. Therfor the puple dide, as it was seid.
Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
14 Forsothe fro that dai in which the kyng hadde comaundid to me, that Y schulde be duyk in the lond of Juda, fro the twentithe yeer `til to the two and threttithe yeer of Artaxerses kyng, bi twelue yeer, Y and my britheren eeten not sustenauncis, that weren due to duykis.
Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
15 But the firste duykis, that weren bifor me, greuyden the puple, and token of hem in breed, and in wiyn, and in monei, ech dai fourti siclis; but also her mynistris oppressiden the puple. Forsothe Y dide not so, for the drede of God;
Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
16 but rather Y bildide in the werk of the wal, and Y bouyte no feeld, and alle my children weren gaderid to the werk.
A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
17 Also `Jewis and the magistratis of hem, an hundrid and fifti men; and thei that camen to me fro hethene men, that ben in oure cumpas, weren in my table.
Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
18 Forsothe bi ech dai oon oxe was maad redi to me, sixe chosun wetheris, outakun volatils, and withynne ten daies dyuerse wynes; and Y yaf many othere thingis; ferthermore and Y axide not the sustenauncis of my duchee; for the puple was maad ful pore.
Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
19 My God, haue thou mynde of me in to good, bi alle thingis whiche Y dide to this puple.
Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.

< Nehemiah 5 >