< Micah 7 >

1 Wo to me, for Y am maad as he that gaderith in heruest rasyns of grapis; there is no clustre for to ete; my soule desiride figis ripe bifore othere.
Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
2 The hooli perischide fro erthe, and riytful is not in men; alle aspien, ether setten tresoun, in blood, a man huntith his brother to deth.
An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
3 The yuel of her hondis thei seien good; the prince axith, and the domesman is in yeldyng; and a greet man spak the desir of his soule, and thei sturbliden togidere it.
Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
4 He that is best in hem, is as a paluyre; and he that is riytful, is as a thorn of hegge. The dai of thi biholdyng, thi visityng cometh, now schal be distriyng of hem.
Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
5 Nyle ye bileue to a frend, and nyle ye truste in a duyk; fro hir that slepith in thi bosum, kepe thou closyngis of thi mouth.
Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
6 For the sone doith wrong to the fadir, and the douyter schal rise ayens hir modir, and the wijf of the sone ayens the modir of hir hosebonde; the enemyes of a man ben the homeli, ether houshold meynee, of hym.
Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
7 Forsothe Y schal biholde to the Lord, Y schal abide God my sauyour; the Lord my God schal here me.
Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
8 Thou, myn enemye, be not glad on me, for Y felle doun, Y schal rise; whanne Y sitte in derknessis, the Lord is my liyt.
Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
9 Y schal bere wraththe of the Lord, for Y haue synned to hym, til he deme my cause, and make my doom; he schal lede out me in to liyt, Y schal se riytwisnesse of hym.
Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
10 And myn enemye schal biholde me, and sche schal be hilid with confusioun, which seith to me, Where is thi Lord God? Myn iyen schulen se hir, now sche schal be in to defoulyng, as clei of stretis.
Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
11 Dai schal come, that thi wallis be bildid; in that dai lawe schal be maad afer.
Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
12 In that dai and Assur schal come til to thee, and `til to stronge citees, and fro stronge citees til to flood; and to see fro see, and to hil fro hil.
A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
13 And erthe schal be in to desolacioun for her dwelleris, and for fruyt of the thouytis of hem.
Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
14 Fede thou thi puple in thi yerde, the floc of thin eritage, that dwellen aloone in wielde wode; in the myddil of Carmel thei schulen be fed of Basan and of Galaad,
Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
15 bi elde daies, bi daies of thi goyng out of the lond of Egipt. Y schal schewe to hym wondurful thingis;
“Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
16 hethene men schulen se, and thei schulen be confoundid on al her strengthe; thei schulen putte hondis on her mouth, the eris of hem schulen be deef;
Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
17 thei schulen licke dust as a serpent; as crepynge thingis of erthe thei schulen be disturblid of her housis; thei schulen not desire oure Lord God, and thei schulen drede thee.
Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
18 God, who is lijk thee, that doist awei wickidnesse, and berist ouer the synne of relifs of thin eritage? He shal no more sende in his stronge veniaunce, for he is willynge merci; he schal turne ayen,
Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
19 and haue merci on vs. He schal put doun oure wickidnessis, and schal caste fer in to depnesse of the see alle oure synnes.
Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
20 Thou schalt yyue treuthe to Jacob, merci to Abraham, whiche thou sworist to oure fadris fro elde daies.
Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.

< Micah 7 >