< Micah 5 >
1 Now thou, douyter of a theef, schalt be distried; thei puttiden on vs bisegyng, in a yerde thei schulen smyte the cheke of the iuge of Israel.
Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
2 And thou, Bethleem Effrata, art litil in the thousyndis of Juda; he that is the lordli gouernour in Israel, schal go out of thee to me; and the goyng out of hym is fro bigynnyng, fro daies of euerlastyngnesse.
“Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
3 For this thing he shal yyue hem til to the tyme in which the trauelinge of child schal bere child, and the relifs of hise britheren schulen be conuertid to the sones of Israel.
Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
4 And he schal stonde, and schal fede in the strengthe of the Lord, in the heiythe of the name of his Lord God; and thei schulen be conuertid, for now he schal be magnefied til to the endis of al erthe.
Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
5 And this schal be pees, whanne Assirius schal come in to oure lond, and whanne he schal trede in oure housis; and we schulen reise on hym seuene scheepherdis, and eiyte primatis men, ether the firste in dignytee.
Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
6 And thei schulen frete the lond of Assur bi swerd, and the lond of Nembroth bi speris of hym; and he schal delyuere vs fro Assur, whanne he schal come in to oure lond, and whanne he schal trede in oure coostis.
Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
7 And relifs of Jacob schulen be in the myddil of many puplis, as dew of the Lord, and as dropis on erbe, whiche abidith not man, and schal not abide sones of men.
Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
8 And relifs of Jacob schulen be in hethene men, in the myddil of many puplis, as a lioun in beestis of the woodis, and as a whelpe of a lioun rorynge in flockis of scheep; and whanne he passith, and defoulith, and takith, there is not that schal delyuere.
Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
9 And thin hond schal be reisid on thin enemyes, and alle thin enemyes schulen perische.
Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
10 And it schal be, in that dai, seith the Lord, Y schal take awei thin horsis fro the myddil of thee, and Y schal distrie thi foure horsid cartis.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
11 And Y schal leese the citees of thi lond, and Y schal distrie alle thi strengthis;
Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
12 and Y schal do awei witchecraftis fro thin hond, and dyuynaciouns schulen not be in thee.
Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
13 And Y schal make for to perische thi `grauun ymagis, and Y schal breke togidere fro the myddil of thee thin ymagis, and thou schalt no more worschipe the werkis of thin hondis.
Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
14 And Y schal drawe out of the middis of thee thi woodis, and Y schal al to-breke thi citees.
Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
15 And Y schal make in woodnesse and indignacioun veniaunce in alle folkis, whiche herden not.
Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”