< Matthew 5 >
1 And Jhesus, seynge the puple, wente vp in to an hil; and whanne he was set, hise disciplis camen to hym.
Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa,
2 And he openyde his mouth, and tauyte hem, and seide,
sai ya fara koya musu. Yana cewa,
3 Blessed ben pore men in spirit, for the kyngdom of heuenes is herne.
“Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu, gama mulkin sama nasu ne.
4 Blessid ben mylde men, for thei schulen welde the erthe.
Masu albarka ne waɗanda suke makoki, gama za a yi musu ta’aziyya.
5 Blessid ben thei that mornen, for thei schulen be coumfortid.
Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u, gama za su gāji duniya.
6 Blessid ben thei that hungren and thristen riytwisnesse, for thei schulen be fulfillid.
Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci, gama za a ƙosar da su.
7 Blessid ben merciful men, for thei schulen gete merci.
Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai, gama za a nuna musu jinƙai.
8 Blessid ben thei that ben of clene herte, for thei schulen se God.
Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya, gama za su ga Allah.
9 Blessid ben pesible men, for thei schulen be clepid Goddis children.
Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci, gama za a kira su’ya’yan Allah.
10 Blessid ben thei that suffren persecusioun for riytfulnesse, for the kingdam of heuenes is herne.
Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci, gama mulkin sama nasu ne.
11 `Ye schulen be blessid, whanne men schulen curse you, and schulen pursue you, and shulen seie al yuel ayens you liynge, for me.
“Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni.
12 Ioie ye, and be ye glad, for youre meede is plenteuouse in heuenes; for so thei han pursued `also profetis that weren bifor you.
Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.
13 Ye ben salt of the erthe; that if the salt vanysche awey, whereynne schal it be saltid? To no thing it is worth ouere, no but that it be cast out, and be defoulid of men.
“Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.
14 Ye ben liyt of the world; a citee set on an hil may not be hid;
“Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa.
15 ne me teendith not a lanterne, and puttith it vndur a busschel, but on a candilstike, that it yyue liyt to alle that ben in the hous.
Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida.
16 So schyne youre liyt befor men, that thei se youre goode werkis, and glorifie youre fadir that is in heuenes.
Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.
17 Nil ye deme, that Y cam to vndo the lawe, or the profetis; Y cam not to vndo the lawe, but to fulfille.
“Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su.
18 Forsothe Y seie to you, til heuene and erthe passe, o lettir or o titel shal not passe fro the lawe, til alle thingis be doon.
Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome.
19 Therfor he that brekith oon of these leeste maundementis, and techith thus men, schal be clepid the leste in the rewme of heuenes; `but he that doith, and techith, schal be clepid greet in the kyngdom of heuenes.
Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama.
20 And Y seie to you, that but your riytfulnesse be more plenteuouse than of scribis and of Farisees, ye schulen not entre into the kyngdom of heuenes.
Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.
21 Ye han herd that it was seid to elde men, Thou schalt not slee; and he that sleeth, schal be gilti to doom.
“Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai; kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’
22 But Y seie to you, that ech man that is wrooth to his brothir, schal be gilti to doom; and he that seith to his brother, Fy! schal be gilti to the counseil; but he that seith, Fool, schal be gilti to the fier of helle. (Geenna )
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna )
23 Therfor if thou offrist thi yifte `at the auter, and ther thou bithenkist, that thi brothir hath sum what ayens thee,
“Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci,
24 leeue there thi yifte bifor the auter, and go first to be recounselid to thi brothir, and thanne thou schalt come, and schalt offre thi yifte.
sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.
25 Be thou consentynge to thin aduersarie soone, while thou art in the weie with hym, lest perauenture thin aduersarie take thee to the domesman, and the domesman take thee to the mynystre, and thou be sent in to prisoun.
“Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku.
26 Treuli Y seie to thee, thou shalt not go out fro thennus, til thou yelde the last ferthing.
Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.
27 Ye han herd that it was seid to elde men, Thou schalt `do no letcherie.
“Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’
28 But Y seie to you, that euery man that seeth a womman for to coueite hir, hath now do letcherie bi hir in his herte.
Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa.
29 That if thi riyt iye sclaundre thee, pulle hym out, and caste fro thee; for it spedith to thee, that oon of thi membris perische, than that al thi bodi go in to helle. (Geenna )
In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
30 And if thi riyt hond sclaundre thee, kitte hym aweye, and caste fro thee; for it spedith to thee that oon of thi membris perische, than that al thi bodi go in to helle. (Geenna )
In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
31 And it hath be seyd, Who euere leeueth his wijf, yyue he to hir a libel of forsakyng.
“An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’
32 But Y seie to you, that euery man that leeueth his wijf, outtakun cause of fornycacioun, makith hir to do letcherie, and he that weddith the forsakun wijf, doith auowtrye.
Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.
33 Eftsoone ye han herd, that it was seid to elde men, Thou schalt not forswere, but thou schalt yelde thin othis to the Lord.
“Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’
34 But Y seie to you, that ye swere not `for ony thing; nethir bi heuene, for it is the trone of God;
Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne;
35 nether bi the erthe, for it is the stole of his feet; nether bi Jerusalem, for it is the citee of a greet kyng; nether thou shalt not swere bi thin heed,
ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne.
36 for thou maist not make oon heere white, ne blacke;
Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba.
37 but be youre word, Yhe, yhe; Nay, nay; and that that is more than these, is of yuel.
Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.
38 Ye han herd that it hath be seid, Iye for iye, and tothe for tothe.
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’
39 But Y seie to you, that ye ayenstonde not an yuel man; but if ony smyte thee in the riyt cheke, schewe to him also the tothir;
Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma.
40 and to hym that wole stryue with thee in doom, and take awey thi coote, leeue thou `to him also thi mantil;
In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma.
41 and who euer constreyneth thee a thousynde pacis, go thou with hym othir tweyne.
In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu.
42 Yyue thou to hym that axith of thee, and turne not awey fro hym that wole borewe of thee.
Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.
43 Ye han herd that it was seid, Thou shalt loue thi neiybore, and hate thin enemye.
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka, ka kuma ƙi abokin gābanka.’
44 But Y seie to you, loue ye youre enemyes, do ye wel to hem that hatiden you, and preye ye for hem that pursuen, and sclaundren you;
Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābankukuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a,
45 that ye be the sones of your fadir that is in heuenes, that makith his sunne to rise vpon goode `and yuele men, and reyneth on iust men and vniuste.
don ku zama’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci.
46 For if ye louen hem that louen you, what mede schulen ye han? whether pupplicans doon not this?
In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba?
47 And if ye greten youre britheren oonli, what schulen ye do more? ne doon not hethene men this?
In kuwa kuna gai da’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba?
48 Therfore be ye parfit, as youre heuenli fadir is parfit.
Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.