< Matthew 4 >
1 Thanne Jhesus was led of a spirit in to desert, to be temptid of the feend.
Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi.
2 And whanne he hadde fastid fourti daies and fourti nyytis, aftirward he hungride.
Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa.
3 And the tempter cam nyy, and seide to hym, If thou art Goddis sone, seie that thes stoones be maad looues.
Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”
4 Which answeride, and seide to hym, It is writun, Not oonli in breed luyeth man, but in ech word that cometh of Goddis mouth.
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’”
5 Thanne the feend took hym in to the hooli citee, and settide hym on the pynacle of the temple,
Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali.
6 and seide to hym, If thou art Goddis sone, sende thee adoun; for it is writun, That to hise aungels he comaundide of thee, and thei schulen take thee in hondis, lest perauenture thou hirte thi foot at a stoon.
Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
7 Eftsoone Jhesus seide to hym, It is writun, Thou shalt not tempte thi Lord God.
Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
8 Eftsoone the feend took hym in to a ful hiy hil, and schewide to hym alle the rewmes of the world, and the ioye of hem;
Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
9 and seide to hym, Alle these `Y schal yyue to thee, if thou falle doun and worschipe me.
Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”
10 Thanne Jhesus seide to hym, Goo, Sathanas; for it is writun, Thou schalt worschipe thi Lord God, and to hym aloone thou shalt serue.
Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’”
11 Thanne the feend lafte hym; and lo! aungels camen nyy, and serueden to hym.
Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.
12 But whanne Jhesus hadde herd that Joon was takun, he wente in to Galilee.
Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili.
13 And he lefte the citee of Nazareth, and cam, and dwelte in the citee of Cafarnaum, biside the see, in the coostis of Zabulon and Neptalym,
Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali
14 that it shulde be fulfillid, that was seid by Ysaie, the profete, seiynge,
don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,
15 The lond of Sabulon and the lond of Neptalym, the weie of the see ouer Jordan, of Galilee of hethen men,
“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun, wannan yankin Galili ta Al’ummai,
16 the puple that walkide in derknessis saye greet liyt, and while men satten in the cuntre of shadewe of deth, liyt aroos to hem.
mutanen da suke zama cikin duhu sun ga babban haske; haske kuma ya haskaka a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”
17 Fro that tyme Jhesus bigan to preche, and seie, Do ye penaunce, for the kyngdom of heuenes schal come niy.
Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
18 And Jhesus walkide bisidis the see of Galilee, and saye twei britheren, Symount, that is clepid Petre, and Andrewe, his brothir, castynge nettis in to the see; for thei weren fischeris.
Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne.
19 And he seide to hem, Come ye aftir me, and Y shal make you to be maad fisscheris of men.
Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.”
20 And anoon thei leften the nettis, and sueden hym.
Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.
21 And he yede forth fro that place, and saie tweyne othere britheren, James of Zebede, and Joon, his brother, in a schip with Zebede, her fadir, amendynge her nettis, and he clepide hem.
Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su,
22 And anoon thei leften the nettis and the fadir, and sueden hym.
nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.
23 And Jhesus yede aboute al Galilee, techynge in the synagogis of hem, and prechynge the gospel of the kyngdom, and heelynge euery languor and eche sekenesse among the puple.
Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane.
24 And his fame wente in to al Sirie; and thei brouyten to hym alle that weren at male ese, and that weren take with dyuerse languores and turmentis, and hem that hadden feendis, and lunatike men, and men in palesy, and he heelide hem.
Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su.
25 And ther sueden hym myche puple of Galile, and of Decapoli, and of Jerusalem, and of Judee, and of biyende Jordan.
Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis, Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.