< Matthew 26 >

1 And it was doon, whanne Jhesus hadde endid alle these wordis, he seide to hise disciplis,
Yayin da Yesu ya gama fadi masu wadannan maganganu, sai ya cewa almajiransa,
2 Ye witen, that aftir twei daies pask schal be maad, and mannus sone schal be bitakun to be crucified.
“Kun sani sauran kwana biyu idin ketarewa ya zo, kuma za'a bada Dan mutum domin a gicciye shi.
3 Than the princes of prestis and the elder men of the puple were gaderid in to the halle of the prince of prestis, that was seid Cayfas,
Sa'annan manyan firistoci da dattawan jama'a suka taru a fadar babban firist, mai suna Kayafa.
4 and maden a counsel to holde Jhesu with gile, and sle him;
Suka shirya yadda zasu kama Yesu a boye su kuma kashe shi.
5 but thei seiden, Not in the haliday, lest perauenture noyse were maad in the puple.
Amma suna cewa, “Ba a lokacin idin ba, domin kada tarzoma ta tashi daga cikin mutane.”
6 And whanne Jhesus was in Betanye, in the hous of Symount leprous,
Sa'adda Yesu yake Baita'anya a gidan Saminu Kuturu,
7 a womman that hadde a box of alabastre of precious oynement, cam to hym, and schedde out on the heed of hym restynge.
daidai lokacin da ya zauna a gefen teburin cin abinci, sai wata mata ta shigo da kwalbar mai, mai tsada, ta zuba wa Yesu a kansa.
8 And disciplis seynge hadden dedeyn, and seiden, Wherto this loss? for it myyte be seld for myche,
Amma da almajiransa suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, “Ina dalilin yin irin wannan asara?
9 and be youun to pore men.
Ai da an sayar da wannan mai da kudi mai yawa a rabawa talakawa.”
10 But Jhesus knewe, and seide to hem, What ben ye heuy to this womman? for sche hath wrouyt in me a good werk.
Amma da yake Yesu ya san tunaninsu, sai yace masu, “Don me kuke damun matar nan? Ta yi abu mai kyau domina.
11 For ye schulen euere haue pore men with you, but ye schulen not algatis haue me.
Kuna da talakawa tare da ku koyaushe, amma ni ba zan kasance da ku ba koyaushe.
12 This womman sendynge this oynement in to my bodi, dide to birie me.
Don a sa'adda ta zuba man nan a jikina, ta yi haka ne don jana'iza ta.
13 Treuli Y seie to you, where euer this gospel schal be prechid in al the world, it schal be seid, that sche dide this, in mynde of hym.
Hakika Ina gaya maku, duk inda za ayi wannan bishara a dukan duniya, abin da matar nan tayi za'a rika ambatar da shi don tunawa da ita.”
14 Thanne oon of the twelue, that was clepid Judas Scarioth, wente forth to the princis of prestis,
Sai daya daga cikin sha biyun, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya tafi wurin manyan firistocin,
15 and seide to hem, What wolen ye yyue to me, and Y schal bitake hym to you? And thei ordeyneden to hym thretti pans of siluer.
yace, ''Me kuke da niyyar bani idan na mika maku shi?” Suka auna masa azurfa talatin.
16 And fro that tyme he souyte oportunyte, to bitraye hym.
Daga wannan lokacin yayi ta neman zarafi da zai bada shi a wurinsu.
17 And in the firste dai of therf looues the disciplis camen to Jhesu, and seiden, Where wolt thou we make redi to thee, to ete paske?
To a rana ta fari na idin ketarewa almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Ina kake so mu shirya maka da zaka ci abincin idin ketarewa?”
18 Jhesus seide, Go ye into the citee to `sum man, and seie to hym, The maistir seith, My tyme is nyy; at thee Y make paske with my disciplis.
Yace, “Ku shiga cikin birnin zaku sami wani mutum sai kuce masa, 'Mallam yace, “lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina.”'''
19 And the disciplis diden, as Jhesus comaundide to hem; and thei maden the paske redi.
Almajiran suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su, suka shirya abincin idin ketarewar.
20 And whanne euentid was come, he sat to mete with hise twelue disciplis.
Da yamma ta yi, sai ya zauna domin ya ci tare da almajiransa goma sha biyu.
21 And he seide to hem, as thei eten, Treuli Y seie to you, that oon of you schal bitraye me.
Sa'adda suke ci, yace, “Hakika ina gaya maku, daya daga cikin ku zai bada ni.”
22 And thei ful sori bigunnen ech bi hym silf to seie, Lord, whether `Y am?
Suka yi bakin ciki, suka fara tambayarsa daya bayan daya, ''Na tabbata ba ni bane ko, Ubangiji?”
23 And he answeride, and seide, He that puttith with me his hoond in the plater, schal bitraye me.
Sai ya amsa, “Wanda ke sa hannu tare da ni cikin kwano daya shi ne zai bada ni.
24 Forsothe mannus sone goith, as it is writun of hym; but wo to that man, bi whom mannus sone schal be bitrayed; it were good to hym, if that man hadde not be borun.
Dan mutum zai tafi, kamar yadda aka rubuta akan sa. Amma kaiton mutumin da ta wurin sa za'a bada Dan mutum! Gwamma da ba'a haifi mutumin nan ba.”
25 But Judas that bitraiede hym, answeride, seiynge, Maister, whether `Y am? Jhesus seide to hym, Thou hast seid.
Yahuza da zai bada shi yace, “Mallam ko ni ne?” Yace masa, “Ka fada da kanka.”
26 And while thei soupeden, Jhesus took breed, and blesside, and brak, and yaf to hise disciplis, and seide, Take ye, and ete; this is my body.
Yayin da suke ci, sai Yesu ya dauki gurasa, ya sa albarka, ya karya. Ya ba almajiran yace, “Ku karba, ku ci, wannan jiki nane.”
27 And he took the cuppe, and dide thankyngis, and yaf to hem,
Sai ya dauki kokon yayi godiya, Ya ba su yace, “Ku sha, dukanku.
28 and seide, Drynke ye alle herof; this is my blood of the newe testament, which schal be sched for many, in to remissioun of synnes.
“Gama wannan jinina ne na alkawari wanda aka zubar domin gafarar zunuban mutane da yawa.
29 And Y seie to you, Y schal not drynke fro this tyme, of this fruyt of the vyne, in to that dai whanne Y schal drynke it newe with you, in the kyngdom of my fadir.
Amma ina gaya maku, ba zan kara shan ruwan inabin nan ba, sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a cikin mulkin Ubana.”
30 And whanne the ympne was seid, thei wenten out in to the mount of Olyuete.
Da suka raira waka, sai suka ka tafi dutsen zaitun.
31 Thanne Jhesus seide to hem, Alle ye schulen suffre sclaundre in me, in this niyt; for it is writun, Y schal smyte the scheeperde, and the scheep of the flok schulen be scaterid.
Sai Yesu yace masu, “Dukan ku zaku yi tuntube a wannan dare sabili da ni, gama a rubuce yake, ''Zan bugi makiyayin, garken tumakin kuma za su watse.'
32 But aftir that Y schal rise ayen, Y schal go bifore you in to Galilee.
Amma bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa Galili.”
33 Petre answeride, and seide to hym, Thouy alle schulen be sclaundrid in thee, Y schal neuer be sclaundrid.
Amma Bitrus yace masa, “Ko dama duka zasu fadi sabili da kai, ni kam bazan fadi ba.”
34 Jhesus seide to him, Treuli Y seie to thee, for in this nyyt bifor the cok crowe, thries thou schalt denye me.
Yesu yace masa, ''Hakika ina gaya maka, a wannan daren kafin carar zakara, za ka yi musun sani na sau uku.”
35 Peter seide to him, Yhe, thouy it bihoue that Y die with thee, Y schal not denye thee. Also alle the disciplis seiden.
Bitrus yace masa, koda zan mutu tare da kai, bazan yi musunka ba.” Sai sauran almajiran suma suka fadi haka.
36 Thanne Jhesus cam with hem in to a toun, that is seid Jessamanye. And he seide to his disciplis, Sitte ye here, the while Y go thider, and preye.
Sa'anna Yesu ya tafi tare da su, wurin da ake kira Getsaimani sai yace wa almajiransa, ''Ku zauna a nan ni kuma zan je gaba in yi addu'a.”
37 And whanne he hadde take Peter, and twei sones of Zebedee, he bigan to be heuy and sori.
Ya dauki Bitrus da kuma 'ya'ya biyu na Zabadi tare da shi, sai ya fara damuwa da juyayi.
38 Thanne he seide to hem, My soule is soreuful to the deeth; abide ye here, and wake ye with me.
Sai yace masu, “Raina na cikin damuwa sosai har ga mutuwa. Ku kasance anan kuna tsaro tare da ni.”
39 And he yede forth a litil, and felde doun on his face, preiynge, and seiynge, My fader, if it is possible, passe this cuppe fro me; netheles not as Y wole, but as thou wolt.
Ya dan taka zuwa gaba kadan, sai ya fadi a fuskarsa, yayi addu'a. Yace, “Ya Ubana, in zai yiwu, bari kokon nan ya wuce ni. Duk da haka, ba nufina za'a bi ba, amma naka nufin.”
40 And he cam to his disciplis, and foond hem slepynge. And he seide to Petir, So, whethir ye myyten not oon our wake with me?
Ya koma wurin almajiran ya same su suna barci, sai ya cewa Bitrus, “Kai, ba zaku yi tsaro tare da ni ba koda sa'a daya?
41 Wake ye, and preye ye, that ye entre not in to temptacioun; for the spirit is redi, but the fleisch is sijk.
Ku yi tsaro kuma, kuyi addu'a domin kada ku fada cikin jaraba. Ruhu dai ya yarda amma, jiki ba karfi.”
42 Eft the secounde tyme he wente, and preyede, seiynge, My fadir, if this cuppe may not passe, but Y drynke hym, thi wille be doon.
Sai ya koma karo na biyu yayi addu'a, Yace, “Ya Ubana, in wannan kokon ba zai wuce ba sai na sha shi, bari nufinka ya kasance.”
43 And eftsoone he cam, and foond hem slepynge; for her iyen weren heuyed.
Ya sake dawowa, ya same su suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi.
44 And he lefte hem, and wente eftsoone, and preiede the thridde tyme, and seide the same word.
Sai ya sake barinsu ya tafi. Ya koma karo na uku yana addu'a yana fadin kalmomi iri daya.
45 Thanne he cam to his disciplis, and seide to hem, Slepe ye now, and reste ye; loo! the our hath neiyed, and mannus sone schal be takun in to the hondis of synneris;
Sai Yesu ya koma wurin almajiran yace masu, “Har yanzu barci kuke kuna hutawa? Duba, lokaci ya kusato, kuma an bada Dan mutum ga hannun masu zunubi.
46 rise ye, go we; loo! he that schal take me, is nyy.
Ku tashi mu tafi. Duba, wanda zai badani ya kusato.”
47 Yit the while he spak, lo! Judas, oon of the twelue, cam, and with hym a greet cumpeny, with swerdis and battis, sent fro the princis of prestis, and fro the eldre men of the puple.
Sa'adda yana cikin magana Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya zo. Babban taro ya zo tare da shi daga wurin manyan firistoci da dattawan jama'a. Suna rike da takubba da kulake.
48 And he that bitraiede hym, yaf to hem a tokene, and seide, Whom euer Y schal kisse, he it is; holde ye hym.
To mutumin da zai bada Yesu ya rigaya ya basu alama, cewa, ''Duk wanda na sumbata, shine. Ku kama shi.''
49 And anoon he cam to Jhesu, and seid, Haile, maister;
Nan da nan ya kaiga Yesu ya ce, “Gaisuwa, Mallam!” sai ya sumbace shi.
50 and he kisside hym. And Jhesus seide to hym, Freend, wherto art thou comun? Thanne thei camen niy, and leiden hoondis on Jhesu, and helden hym.
Yesu kuwa yace masa, “Aboki, kayi abin da ya kawo ka.” Sai suka iso suka sa hannuwansu kan Yesu suka kama shi.
51 And lo! oon of hem that weren with Jhesu, streiyte out his hoond, and drouy out his swerd; and he smoot the seruaunt of the prince of prestis, and kitte of his ere.
Nan take, daya daga cikin wadanda suke tare da Yesu ya mika hannunsa, ya zare takobinsa, ya sare wa bawan babban firist din kunne.
52 Thanne Jhesus seide to hym, Turne thi swerd in to his place; for alle that taken swerd, schulen perische bi swerd.
Sai Yesu yace, masa, “Ka maida takobinka cikin kubensa, domin duk wadanda suka dauki takobi su ma ta wurin takobi za su hallaka.
53 Whether gessist thou, that Y may not preie my fadir, and he schal yyue to me now mo than twelue legiouns of aungels?
Ko kana tunanin ba zan iya kiran Ubana ba, ya kuma aiko da rundunar Mala'iku fiye da goma sha biyu?
54 Hou thanne schulen the scriptures be fulfilled? for so it bihoueth to be doon.
Amma to tayaya za'a cika nassi, cewa dole wannan ya faru?''
55 In that our Jhesus seide to the puple, As to a theef ye han gon out, with swerdis and battis, to take me; dai bi dai Y sat among you, and tauyt in the temple, and ye helden me not.
A wannan lokacin Yesu yace wa taron, “Kun zo da takubba da kulake ku kama ni kamar dan fashi? Ina zaune kowace rana a haikali ina koyarwa, amma baku kama ni ba.
56 But al this thing was don, that the scripturis of profetis schulden be fulfillid. Thanne alle the disciplis fledden, and leften hym.
Amma duk wannan ya faru ne don a cika abinda annabawa suka rubuta.” Bayan haka sai dukkan almajiran suka bar shi suka gudu.
57 And thei helden Jhesu, and ledden hym to Cayfas, the prince of prestis, where the scribis and the Farisees, and the eldre men of the puple weren comun togidere.
Wadanda suka kama Yesu, suka kai shi wurin Kayafa babban firist, inda marubuta da duttawan jama'a suka taru.
58 But Petir swede him afer, in to the halle of the prince of prestis; and he wente in, and sat with the seruauntis, to se the ende.
Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har zuwa farfajiyar babban firist din. Ya shiga ya zauna da masu tsaro domin ya ga abinda zai faru.
59 And the prince of prestis, and al the counsel souyten fals witnessing ayens Jhesu, that thei schulden take hym to deeth;
A wannan lokaci manyan firistoci da duk 'yan majalisar suka fara neman shaidar karya akan Yesu, domin su samu su kashe shi.
60 and thei founden not, whanne manye false witnessis weren comun. But at the laste, twei false witnessis camen,
Amma ba su samu ko daya ba, ko dayake an samu shaidun karya dayawa da suka gabata. Amma daga baya sai wasu su biyu suka fito
61 and seiden, `This seide, Y may distruye the temple of God, and after the thridde dai bilde it ayen.
sukace ''Wannan mutum yace zan iya rushe haikalin Allah, in kuma gina shi cikin kwana uku.'''
62 And the prince of prestis roos, and seide to hym, Answerist thou no thing to tho thingis, that these witnessen ayens thee?
Babban Firist din ya tashi tsaye yace masa, “Ba zaka ce komai ba? Wace irin shaida ce ake yi akanka?”
63 But Jhesus was stille. And the prince of prestis seide to hym, Y coniure thee bi lyuynge God, that thou seie to vs, if thou art Crist, the sone of God.
Amma Yesu yayi shiru. Babban Firist ya ce, “Na umarce ka da sunan Allah mai rai, ka gaya mana ko kai Almasihu ne, Dan Allah.''
64 Jhesus seide to him, Thou hast seid; netheles Y seie to you, `fro hennus forth ye schulen se mannus sone sittinge at the riythalf of the vertu of God, and comynge in the cloudis of heuene.
Yesu ya amsa masa, “Ka fada da bakin ka. Amma ina gaya maka, daga yanzu zaka ga Dan mutun na zaune a hannun dama na iko, ya na zuwa akan gizagizai na sama.”
65 Thanne the prince of prestis to-rente his clothis, and seide, He hath blasfemed; what yit han we nede to witnessis? lo! now ye han herd blasfemye; what semeth to you?
Sai babban firist din ya yayyaga rigarsa, yana cewa, “Yayi sabo! don me ku ke neman wata shaida kuma? Duba, yanzu kun ji sabon.
66 And thei answeriden, and seiden, He is gilti of deeth.
Menene tunaninku?” Suka amsa sukace, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Thanne thei speten `in to his face, and smyten hym with buffatis; and othere yauen strokis with the pawme of her hondis in his face,
Sai suka tofa masa yawu a fuska, suka kuma yi masa duka, suka kuma mammare shi da tafin hannuwansu,
68 and seide, Thou Crist, arede to vs, who is he that smoot thee?
sukace, ''Ka yi mana anabci, kai Almasihu. Wanene wanda ya dokeka.
69 And Petir sat with outen in the halle; and a damysel cam to hym, and seide, Thou were with Jhesu of Galilee.
To Bitrus kuwa na zaune a farfajiyar, sai wata yarinya baiwa ta zo wurinsa tana cewa, “Kaima kana tare da Yesu na Galili.”
70 And he denyede bifor alle men, and seide, Y woot not what thou seist.
Amma ya yi musun haka a gaban su duka, yace, “Ban ma san abinda kike magana akai ba.”
71 And whanne he yede out at the yate, another damysel say hym, and seide to hem that weren there, And this was with Jhesu of Nazareth.
Da ya fita zuwa bakin kofa, nan ma wata yarinyar baiwa ta gan shi tace wa wadanda suke wurin, “Wannan mutumin ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 And eftsoone he denyede with an ooth, For I knewe not the man.
Sai yayi musun haka kuma, har da rantsuwa, yace, “Ban san mutumin nan ba.”
73 And a litil aftir, thei that stooden camen, and seiden to Petir, Treuli thou art of hem; for thi speche makith thee knowun.
Bayan dan lokaci kadan wadanda suke a tsaye suka zo wurin Bitrus suka ce masa, “Hakika kai daya daga cikin su ne, gama harshen ka ya tonaka.”
74 Thanne he bigan to warie and to swere, that he knewe not the man. And anoon the cok crewe.
Sai ya fara rantsuwa irin ta la'ana, yana cewa, ''Ban san wannan mutumin ba,” nan da nan zakara yayi cara.
75 And Petir bithouyte on the word of Jhesu, that he hadde seid, Bifore the cok crowe, thries thou schalt denye me. And he yede out, and wepte bitterli.
Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya fada, “Kafin carar zakara zaka yi musun sani na sau uku.” Sai ya fita waje yayi kuka mai zafi.''

< Matthew 26 >