< Matthew 21 >

1 And whanne Jhesus cam nyy to Jerusalem, and cam to Bethfage, at the mount of Olyuete, thanne sente he his twei disciplis, and seide to hem,
Yayinda Yesu da almajiransa suka kusato Urushalima sai suka zo Betafaji wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa guda biyu,
2 Go ye in to the castel that is ayens you, and anoon ye schulen fynde an asse tied, and a colt with hir; vntien ye, and brynge to me.
yace masu, “Ku shiga kauyen da yake gaban ku zaku iske wata jaka da aholaki tara da ita. Ku kwance su ku kawo mani su.
3 And if ony man seie to you ony thing, seie ye, that the Lord hath nede to hem; and anoon he schal leeue hem.
Idan wani ya gaya maku wani abu game da haka, sai ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsu,' mutumin kuwa zai aiko ku da su nan da nan.”
4 Al this was doon, that that thing schulde be fulfillid, that was seid bi the prophete, seiynge, Seie ye to the douyter of Syon, Lo!
Anyi wannan kuwa domin a cika annabcin anabin. Yace,
5 thi kyng cometh to thee, meke, sittynge on an asse, and a fole of an asse vnder yok.
“Ku cewa diyar Sihiyona, duba, ga sarkinki na zuwa wurin ki, mai tawali'u ne, kuma akan jaki wanda aholaki ne.”
6 And the disciplis yeden, and diden as Jhesus comaundide hem.
Sai almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 And thei brouyten an asse, and the fole, and leiden her clothis on hem, and maden hym sitte aboue.
Suka kawo jakar da dan aholakin, suka sa tufafinsu akai, Yesu kuwa ya zauna akan tufafin.
8 And ful myche puple strewiden her clothis in the weie; othere kittiden braunchis of trees, and strewiden in the weie.
Yawancin jama'a kuwa suka baza tufafinsu akan hanya, wasu kuma suka yanko ganye daga bishiyoyi suka shimfida su a hanya.
9 And the puple that wente bifore, and that sueden, crieden, and seiden, Osanna to the sone of Dauid; blessid is he that cometh in the name of the Lord; Osanna in hiy thingis.
Taron jama'a da suke gabansa da wadanda suke bayansa, suka ta da murya suna cewa, “Hossana ga dan Dauda! mai albarka ne shi wanda ke zuwa cikin sunan Ubangiji. Hossana ga Ubangiji!”
10 And whanne he was entrid in to Jerusalem, al the citee was stirid, and seide, Who is this?
Sa'adda Yesu ya shiga Urushalima sai doki ya cika birnin ana cewa, “Wanene wannan?”
11 But the puple seide, This is Jhesus, the prophete, of Nazareth of Galilee.
Sai jama'a suka amsa, “Wannan shine Yesu annabi, daga Nazaret ta Galili.”
12 And Jhesus entride in to the temple of God, and castide out of the temple alle that bouyten and solden; and he turnede vpsedoun the bordis of chaungeris, and the chayeris of men that solden culueris.
Sai Yesu ya shiga haikalin. Ya kori duk wadanda ke saye da sayarwa a cikin ikiilisiya. Ya birkice teburan masu canjin kudi da kujerun masu sayar da tantabaru.
13 And he seith to hem, It is writun, Myn hous schal be clepid an hous of preier; but ye han maad it a denne of theues.
Ya ce masu, “A rubuce yake, 'Za a kira gidana gidan addu'a,' amma kun mayar dashi kogon 'yan fashi.”
14 And blynde and crokid camen to hym in the temple, and he heelide hem.
Sai makafi da guragu suka zo wurin sa a haikalin, ya warkar da su.
15 But the princis of prestis and scribis, seynge the merueilouse thingis that he dide, and children criynge in the temple, and seiynge, Osanna to the sone of Dauid, hadden indignacioun,
Amma da manyan firistoci da malaman attaura suka ga abubuwan banmamaki da yayi, kuma sa'adda suka ji yara suna tada murya a cikin haikalin suna cewa, “Hossana ga dan Dauda,” sai suka ji haushi.
16 and seiden to hym, Herist thou what these seien? And Jhesus seide to hem, Yhe; whether ye han neuer redde, That of the mouth of yonge children, and of soukynge childryn, thou hast maad perfit heriyng?
Suka ce masa, kana jin abinda wadannan mutanen ke fadi?'' Yesu ya ce masu, “I! Amma ba ku taba karantawa ba, 'daga bakin jarirai da masu shan mama ka sa yabo'?”
17 And whanne he hadde left hem, he wente forth out of the citee, in to Bethanye; and there he dwelte, and tauyte hem of the kyngdom of God.
Sai Yesu ya bar su, ya fice daga birnin zuwa Betaniya ya kwana a wurin.
18 But on the morowe, he, turnynge ayen in to the citee, hungride.
Washegari da safe yayin da yake komawa birnin, sai yaji yunwa.
19 And he saye a fige tree bisidis the weie, and cam to it, and foond no thing ther ynne but leeues oneli. And he seide to it, Neuer fruyt come forth of thee, in to with outen eende, And anoon the fige tre was dried vp. (aiōn g165)
Da ya ga bishiyar baure a bakin hanya, sai yaje wurin amma bai sami kome ba sai dai ganye. Sai ya ce mata, “Kada ki kara yin 'ya'ya har abada.” Sai nan take bishiyar bauren ta bushe. (aiōn g165)
20 And disciplis `sawen, and wondriden, seiynge, Hou anoon it driede.
Da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suka ce, “Kaka bishiyar bauren ta bushe nan da nan?”
21 And Jhesus answeride, and seide to hem, Treuli Y seie to you, if ye haue feith, and douten not, not oonli ye schulen do of the fige tree, but also if ye seyn to this hil, Take, and caste thee in to the see, it schal be don so.
Yesu ya amsa yace masu, “Hakika ina ce maku, in dai kuna da bangaskiya ba ku yi shakka ba, ba abinda aka yi wa bauren nan kadai za kuyi ba har ma za ku cewa tsaunin nan, “Ka ciru ka fada teku,' sai kuwa haka ta kasance.
22 And alle thingis what euere ye bileuynge schulen axe in preyer, ye schulen take.
Kome kuka roka cikin addu'a, in dai kun gaskanta, za ku samu.”
23 And whanne he cam in to the temple, the princis of prestis and elder men of the puple camen to hym that tauyte, and seiden, In what power doist thou these thingis? and who yaf thee this power?
Sa'adda Yesu ya shiga haikalin, sai manyan fristocin da shugabannin jama'a suka zo suka same shi yayin da yake koyarwa, suka ce, “Da wane iko kake yin wadannan abubuwa?”
24 Jhesus answeride, and seide to hem, And Y schal axe you o word, the which if ye tellen me, Y schal seie to you, in what power Y do these thingis.
Yesu ya amsa yace masu, “Ni ma zan yi maku tambaya daya. In kun fada mani, ni ma zan fada maku ko da wane iko nake yin wadannan abubuwa.
25 Of whennys was the baptym of Joon; of heuene, or of men? And thei thouyten with ynne hem silf,
Daga ina baftismar Yahaya ta fito, daga sama ko kuma daga mutune?” Sai suka yi shawara a tsakanin su, suka ce, “In munce, 'daga sama,' zai ce mana, 'don me bamu gaskanta dashi ba?'
26 seiynge, If we seien of heuene, he schal seie to vs, Whi thanne bileuen ye not to hym? If we seien of men, we dreden the puple, for alle hadden Joon as a prophete.
Amma in munce, ' daga mutune,' muna tsoron jama'a, saboda sun san Yahaya annabi ne.”
27 And thei answeriden to Jhesu, and seiden, We witen not. And he seide to hem, Nether Y seie to you, in what power Y do these thingis.
Sai suka amsa ma Yesu suka ce, ''Bamu sani ba.” Shi ma yace masu, “Nima bazan gaya maku ko da wane iko nake yin abubuwan nan ba.
28 But what semeth to you? A man hadde twey sones; and he cam to the firste, and seide, Sone, go worche this dai in my vyneyerd.
Amma me kuke tunani? Wani mutum yana da 'ya'ya biyu. Ya je wurin na farkon yace, 'Da, je ka kayi aiki yau a cikin gona.'
29 And he answeride, and seide, Y nyle; but afterward he forthouyte, and wente forth.
Yaron ya amsa yace, 'bazan yi ba,' amma daga baya ya canza tunaninsa ya tafi.
30 But he cam to `the tother, and seide on lijk maner. And he answeride, and seide, Lord, Y go; and he wente not.
Sai mutumin ya je wurin da na biyun ya fada masa abu guda. Wannan dan ya amsa ya ce, 'zanje, baba,' amma bai je ba.
31 Who of the tweyne dide the fadris wille? Thei seien to hym, The firste. Jhesus seith to hem, Treuli Y seie to you, for pupplicans and hooris schulen go bifor you `in to the kyngdom of God.
Wanene a cikin 'ya'ya biyun nan yayi nufin ubansa?” Suka ce, “na farkon.” Yesu ya ce masu, “Hakika ina gaya maku, masu karbar haraji da karuwai za su shiga mulkin Allah kafin ku.
32 For Joon cam to you in the weie of riytwisnesse, and ye bileueden not to him; but pupplicans and hooris bileueden to hym. But ye sayn, and hadden no forthenkyng aftir, that ye bileueden to hym.
Gama Yahaya ya zo maku a hanyar adalci, amma ba ku gaskata da shi ba, a yayinda masu karbar haraji da karuwai suka gaskata da shi. Ku kuwa, bayan kun ga abin da ya faru, baku ma tuba daga baya ba don ku gaskata da shi.
33 Here ye another parable. There was an hosebonde man, that plauntide a vynyerd, and heggide it aboute, and dalfe a presour ther ynne, and bildide a tour, and hiride it to erthe tilieris, and wente fer in pilgrimage.
Ku saurari wani misalin. Anyi wani mutum, mai gona. Yayi shuka a gonar, ya shinge ta, ya gina ramin matse inabi a cikin gonar, ya kuma gina wata hasumiyar tsaro, sai ya bada hayar gonar ga wadansu manoma. Sai ya tafi wata kasa.
34 But whanne the tyme of fruytis neiyede, he sente his seruauntis to the erthe tilieris, to take fruytis of it.
Da kakar inabi ta yi, sai ya aiki wadansu bayi su karbo masa amfanin gonar.
35 And the erthetilieris token his seruauntis, and beeten `the toon, thei slowen another, and thei stonyden another.
Amma manoman suka kama bayin, suka doddoki dayan, suka kashe dayan, suka jejjefe dayan da duwatsu.
36 Eftsoone he sente othere seruauntis, mo than the firste, and in lijk maner thei diden to hem.
Sai mai gonar ya sake aika wadansu bayinsa da suka fi na farko, amma manoman suka yi masu kamar yadda suka yi wa sauran.
37 And at the laste he sente his sone to hem, and seide, Thei schulen drede my sone.
Bayan wannnan, sai mai gonar ya aika da dansa wurin su yana cewa, 'za su yi wa dana biyayya.'
38 But the erthe tilieris, seynge the sone, seiden with ynne hem silf, This is the eire; come ye, sle we hym, and we schulen haue his eritage.
Amma da manoman suka ga dan, sai suka ce a tsakanin su, 'wannan shine magajin. Kuzo, mu kashe shi mu gaji gonar.'
39 And thei token, and castiden hym out of the vynyerd, and slowen hym.
Sai suka dauke shi, suka jefar da shi daga cikin gonar, suka kashe shi.
40 Therfor whanne the lord of the vyneyerd schal come, what schal he do to thilke erthe tilieris?
To idan me gonar ya zo, me zai yiwa manoman?
41 Thei seien to hym, He schal leese yuele the yuele men, and he schal sette to hire his vyneyerd to othere erthetilieris, whyche schulen yelde to hym fruyt in her tymes.
Suka ce masa, “Zai hallaka mugayen manoman nan ta hanya mai tsanani, zai kuma bada gonar haya ga wadansu manoman, mutanen da za su biya, lokacin da inabin ya nuna.”
42 Jhesus seith to hem, Redden ye neuer in scripturis, The stoon which bilderis repreueden, this is maad in to the heed of the corner? Of the Lord this thing is don, and it is merueilous bifor oure iyen.
Yesu yace masu, “Baku taba karantawa a nassi ba,'' 'Dutsen da magina suka ki ya zama dutse mafi amfani. Wannan daga Ubangijine, kuma abin mamaki ne a idanunmu?'
43 Therfor Y seie to you, that the kyngdom of God schal be takun fro you, and shal be youun to a folc doynge fruytis of it.
Saboda haka ina gaya maku, za a karbe mulkin Allah daga wurin ku a ba wata al'umma da zata bada amfaninsa.
44 And he that schal falle on this stoon, schal be brokun; but on whom it schal falle, it schal al tobrise hym.
Duk wanda ya fadi akan dutsen nan zai ragargaje. Amma duk wanda dutsen ya fadawa, zai nike.”
45 And whanne the princes of prestis and Farisees hadden herd hise parablis, thei knewen that he seide of hem.
Da manyan firistocin da farisawan suka ji wannan misalin, sai suka gane da su yake.
46 And thei souyten to holde hym, but thei dredden the puple, for thei hadden hym as a prophete.
Da suka nemi kama shi, sai suka ji tsoron taron, saboda mutanen sun dauke shi annabi.

< Matthew 21 >