< Matthew 17 >

1 And after sixe daies Jhesus took Petre, and James, and Joon, his brother, and ledde hem aside in to an hiy hil,
Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
2 and was turned in to an othir licnesse bifor hem. And his face schone as the sunne; and hise clothis weren maad white as snowe.
A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
3 And lo! Moises and Elie apperiden to hem, and spaken with hym.
Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
4 And Petre answeride, and seide to Jhesu, Lord, it is good vs to be here. If thou wolt, make we here thre tabernaclis; to thee oon, to Moises oon, and oon to Elye. Yit the while he spak, lo!
Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
5 a briyt cloude ouerschadewide hem; and lo! a voice out of the cloude, that seide, This is my dereworth sone, in whom Y haue wel pleside to me; here ye hym.
Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
6 And the disciplis herden, and felden doun on her faces, and dredden greetli.
Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
7 And Jhesus cam, and touchide hem, and seide to hem, Rise vp, and nyle ye drede.
Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
8 And thei liften vp her iyen, and saien no man, but Jhesu aloone.
Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
9 And as thei camen doun of the hille, Jhesus comaundide to hem, and seide, Seie ye to no man the visioun, til mannus sone rise ayen fro deeth.
Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
10 And his disciplis axiden hym, and seiden, What thanne seien the scribis, that it bihoueth that Elie come first?
Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
11 He answeride, and seide to hem, Elie schal come, and he schal restore alle thingis.
Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
12 And Y seie to you, that Elie is nowe comun, and thei knewen hym not, but thei diden in him what euer thingis thei wolden; and so mannus sone schal suffre of hem.
Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
13 Thanne the disciplis vndurstoden, that he seide to hem of Joon Baptist.
Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
14 And whanne he cam to the puple, a man cam to hym, and felde doun on hise knees bifor hym, and seide,
Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
15 Lord, haue merci on my sone; for he is lunatike, and suffrith yuele, for ofte tymes he fallith in to the fier, and ofte tymes in to water.
Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
16 And Y brouyte hym to thi disciplis, and thei myyten not heele hym.
Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
17 Jhesus answeride, and seide, A! thou generacion vnbileueful and weiward; hou long schal Y be with you? hou long schal Y suffre you? Brynge ye hym hider to me.
Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
18 And Jhesus blamede hym, and the deuel wente out fro hym; and the child was heelid fro that our.
Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
19 Thanne the disciplis camen to Jhesu priueli, and seiden to hym, Whi myyten not we caste hym out?
Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
20 Jhesus seith to hem, For youre vnbileue. Treuli Y seie to you, if ye han feith, as a corn of seneueye, ye schulen seie to this hil, Passe thou hennus, and it schal passe; and no thing schal be vnpossible to you;
Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
21 but this kynde is not caste out, but bi preiyng and fastyng.
22 And whilis thei weren abidynge togidere in Galilee, Jhesus seide to hem, Mannus sone schal be bitraied in to the hondis of men;
Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
23 and thei schulen sle hym, and the thridde day he schal rise ayen to lijf. And thei weren ful sori.
Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
24 And whanne thei camen to Cafarnaum, thei that token tribute, camen to Petre, and seiden to hym, Youre maister payeth not tribute?
Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
25 And he seide, Yhis. And whanne he was comen in to the hous, Jhesus cam bifor hym, and seide, Symount, what semeth to thee? Kyngis of erthe, of whom taken thei tribute? of her sones, ether of aliens?
Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
26 And he seide, Of aliens. Jhesus seide to hym, Thanne sones ben fre.
Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
27 But that we sclaundre hem not, go to the see, and caste an hook, and take thilke fisch that first cometh vp; and, whanne his mouth is opened, thou schalt fynde a stater, and yyue for thee and for me.
Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”

< Matthew 17 >