< Mark 6 >

1 And he yede out fro thennus, and wente in to his owne cuntre; and hise disciplis folewiden him.
Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
2 And whanne the sabat was come, Jhesus bigan to teche in a synagoge. And many herden, and wondriden in his techyng, and seiden, Of whennus to this alle these thingis? and what is the wisdom that is youun to hym, and siche vertues whiche ben maad bi hise hondis?
Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
3 Whether this is not a carpenter, the sone of Marie, the brother of James and of Joseph and of Judas and of Symount? whether hise sistris ben not here with vs? And thei weren sclaundrid in hym.
Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
4 And Jhesus seide to hem, That a profete is not without onoure, but in his owne cuntrey, and among his kynne, and in his hous.
Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
5 And he myyte not do there ony vertu, saue that he helide a fewe sijk men, leiynge on hem hise hoondis.
Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
6 And he wondride for the vnbileue of hem. And he wente aboute casteles on ech side, and tauyte.
Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7 And he clepide togidere twelue, and bigan to sende hem bi two togidere; and yaf to hem power of vnclene spiritis,
Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
8 and comaundide hem, that thei schulde not take ony thing in the weie, but a yerde oneli, not a scrippe, ne breed, nether money in the girdil,
ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
9 but schod with sandalies, and that thei schulden not be clothid with twei cootis.
sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10 And he seide to hem, Whidur euer ye entren in to an hous, dwelle ye there, til ye goon out fro thennus.
Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
11 And who euer resseyueth you not, ne herith you, go ye out fro thennus, and schake awei the powdir fro youre feet, in to witnessyng to hem.
Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12 And thei yeden forth, and prechiden, that men schulden do penaunce.
Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
13 And thei castiden out many feendis, and anoyntiden with oyle many sijk men, and thei weren heelid.
Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14 And kyng Eroude herde, for his name was maad opyn, and seide, That Joon Baptist hath risen ayen fro deeth, and therfor vertues worchen in hym.
Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
15 Othir seiden, That it is Helie; but othir seiden, That it is a profete, as oon of profetis.
Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
16 And whanne this thing was herd, Eroude seide, This Joon, whom Y haue biheedide, is risun ayen fro deeth.
Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
17 For thilke Eroude sente, and helde Joon, and boond hym in to prisoun, for Erodias, the wijf of Filip, his brothir; for he hadde weddid hir.
Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18 For Joon seide to Eroude, It is not leueful to thee, to haue the wijf of thi brothir.
Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
19 And Erodias leide aspies to hym, and wolde sle hym, and myyte not.
Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
20 And Eroude dredde Joon, and knewe hym a iust man and hooli, and kepte hym. And Eroude herde hym, and he dide many thingis, and gladli herde hym.
Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21 And whanne a couenable dai was fallun, Eroude in his birthdai made a soper to the princis, and tribunes, and to the grettest of Galilee.
Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
22 And whanne the douyter of thilke Erodias was comun ynne, and daunside, and pleside to Eroude, and also to men that saten at the mete, the kyng seide to the damysel, Axe thou of me what thou wolt, and Y schal yyue to thee.
Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
23 And he swore to hir, That what euer thou axe, Y schal yyue to thee, thouy it be half my kyngdom.
Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
24 And whanne sche hadde goon out, sche seide to hir modir, What schal Y axe? And sche seide, The heed of Joon Baptist.
Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
25 And whanne sche was comun ynne anoon with haast to the kyng, sche axide, and seide, Y wole that anoon thou yyue to me in a dische the heed of Joon Baptist.
Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
26 And the kyng was sori for the ooth, and for men that saten togidere at the meete he wolde not make hir sori;
Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
27 but sente a manqueller and comaundide, that Joones heed were brouyt in a dissche. And he bihedide hym in the prisoun,
Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
28 and brouyte his heed in a disch, and yaf it to the damysel, and the damysel yaf to hir modir.
Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
29 And whanne this thing was herd, hise disciplis camen, and token his bodi, and leiden it in a biriel.
Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30 And the apostlis camen togidere to Jhesu, and telden to hym alle thingis, that thei hadden don, and tauyt.
Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
31 And he seide to hem, Come ye bi you silf in to a desert place; and reste ye a litil. For there were many that camen, and wenten ayen, and thei hadden not space to ete.
Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
32 And thei yeden in to a boot, and wenten in to a desert place bi hem silf.
Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33 And thei sayn hem go awei, and many knewen, and thei wenten afoote fro alle citees, and runnen thidur, and camen bifor hem.
Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
34 And Jhesus yede out, and saiy myche puple, and hadde reuth on hem, for thei weren as scheep not hauynge a scheepherd. And he bigan to teche hem many thingis.
Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35 And whanne it was forth daies, hise disciplis camen, and seiden, This is a desert place, and the tyme is now passid;
Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
36 lete hem go in to the nexte townes and villagis, to bie hem meete to ete.
Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37 And he answeride, and seide to hem, Yyue ye to hem to ete. And thei seiden to hym, Go we, and bie we looues with two hundrid pens, and we schulen yyue to hem to ete.
Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
38 And he seith to hem, Hou many looues han ye? Go ye, and se. And whanne thei hadden knowe, thei seien, Fyue, and two fischis.
Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
39 And he comaundide to hem, that thei schulden make alle men sitte to mete bi cumpanyes, on greene heye.
Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
40 And thei saten doun bi parties, bi hundridis, and bi fifties.
Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
41 And whanne he hadde take the fyue looues, and twei fischis, he biheelde in to heuene, and blesside, and brak looues, and yaf to hise disciplis, that thei schulden sette bifor hem. And he departide twei fischis to alle;
Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42 and alle eeten, and weren fulfillid.
Dukansu suka ci suka koshi.
43 And thei token the relifs of brokun metis, twelue cofyns ful, and of the fischis.
Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
44 And thei that eeten, weren fyue thousynde of men.
Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45 And anoon he maad hise disciplis to go up in to a boot, to passe bifor hym ouer the se to Bethsaida, the while he lefte the puple.
Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
46 And whanne he hadde left hem, he wente in to an hille, to preye.
Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
47 And whanne it was euen, the boot was in the myddil of the see, and he aloone in the loond;
Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48 and he say hem trauelynge in rowyng; for the wynde was contrarie to hem. And aboute the fourthe wakynge of the nyyt, he wandride on the see, and cam to hem, and wolde passe hem.
Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
49 And as thei sayn hym wandrynge on the see, thei gessiden that it weren a fantum, and crieden out;
Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
50 for alle sayn hym, and thei weren afraied. And anoon he spak with hem, and seide to hem, Triste ye, Y am; nyle ye drede.
gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
51 And he cam vp to hem in to the boot, and the wynde ceesside. And thei wondriden more `with ynne hem silf;
Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
52 for thei vndurstoden not of the looues; for her herte was blyndid.
Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53 And whanne thei weren passid ouer the see, thei camen in to the lond of Genasareth, and settiden to loond.
Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
54 And whanne thei weren gon out of the boot, anoon thei knewen hym.
Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
55 And thei ranne thorou al that cuntre, and bigunnen to brynge sijk men in beddis on eche side, where thei herden that he was.
Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56 And whidur euer `he entride in to villagis, ethir in to townes, or in to citees, thei setten sijk men in stretis, and preiden hym, that thei schulden touche namely the hemme of his cloth; and hou many that touchiden hym, weren maad saaf.
Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

< Mark 6 >