< Mark 13 >
1 And whanne he wente out of the temple, oon of hise disciplis seide to hym, Maister, biholde, what maner stoonys, and what maner bildyngis.
da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
2 And Jhesu answeride, and seide to hym, Seest thou alle these grete bildingis? ther schal not be left a stoon on a stoon, which schal not be distried.
Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
3 And whanne he sat in the mount of Olyues ayens the temple, Petir and James and Joon and Andrew axiden hym bi hem silf,
Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
4 Seie thou to vs, whanne these thingis schulen be don, and what tokene schal be, whanne alle these thingis schulen bigynne to be endid.
Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
5 And Jhesus answeride, and bigan to seie to hem, Loke ye, that no man disseyue you;
Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
6 for manye schulen come in my name, seiynge, That Y am; and thei schulen disseyue manye.
Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7 And whanne ye here batels and opynyouns of batels, drede ye not; for it bihoueth these thingis to be doon, but not yit anoon is the ende.
In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
8 For folk schal rise on folk, and rewme on rewme, and erthe mouyngis and hungur schulen be bi placis; these thingis schulen be bigynnyngis of sorewis.
Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9 But se ye you silf, for thei schulen take you in counsels, and ye schulen be betun in synagogis; and ye schulen stonde bifor kyngis and domesmen for me, in witnessyng to hem.
Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
10 And it bihoueth, that the gospel be first prechid among al folk.
Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11 And whanne thei taken you, and leden you forth, nyle ye bifore thenke what ye schulen speke, but speke ye that thing that schal be youun to you in that our; for ye ben not the spekeris, but the Hooli Goost.
Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
12 For a brother schal bitake the brother in to deth, and the fadir the sone, and sones schulen rise togider ayens fadris and modris, and punysche hem bi deeth.
Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
13 And ye schulen be in hate to alle men for my name; but he that lastith in to the ende, schal be saaf.
Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14 But whanne ye schulen se the abhomynacioun of discoumfort, stondynge where it owith not; he that redith, vndurstonde; thanne thei that be in Judee, fle `in to hillis.
Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
15 And he that is aboue the roof, come not doun in to the hous, nethir entre he, to take ony thing of his hous;
Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
16 and he that schal be in the feeld, turne not ayen bihynde to take his cloth.
Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17 But wo to hem that ben with child, and norischen in tho daies.
Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
18 Therfor preye ye, that thei be not don in wyntir.
Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
19 But thilke daies of tribulacioun schulen be suche, whiche maner weren not fro the bigynnyng of creature, which God hath maad, til now, nethir schulen be.
A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
20 And but the Lord hadde abredgide tho daies, al fleische hadde not be saaf; but for the chosun whiche he chees, the Lord hath maad schort the daies.
In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21 And thanne if ony man seie to you, Lo! here is Crist, lo! there, bileue ye not.
To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
22 For false Cristis and false prophetis schulen rise, and schulen yyue tokenes and wondris, to disseyue, if it may be don, yhe, hem that be chosun.
Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
23 Therfor take ye kepe; lo! Y haue bifor seid to you alle thingis.
Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24 But in tho daies, aftir that tribulacioun, the sunne schal be maad derk, and the moon schal not yyue hir liyt,
Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
25 and the sterris of heuene schulen falle doun, and the vertues that ben in heuenes, schulen be moued.
Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
26 And thanne thei schulen se mannus sone comynge in cloudis of heuene, with greet vertu and glorie.
Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
27 And thanne he schal sende hise aungelis, and schal geder hise chosun fro the foure wyndis, fro the hiyest thing of erthe til to the hiyest thing of heuene.
Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28 But of the fige tree lerne ye the parable. Whanne now his braunche is tendre, and leeues ben sprongun out, ye knowen that somer is nyy.
“Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
29 So whanne ye seen these thingis be don, wite ye, that it is nyy in the doris.
Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30 Treuli Y seie to you, that this generacioun schal not passe awei, til alle these thingis be don.
Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
31 Heuene and erthe schulen passe, but my wordis schulen not passe.
Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
32 But of that dai or our no man woot, nether aungels in heuene, nether the sone, but the fadir.
Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33 Se ye, wake ye, and preie ye; for ye witen not, whanne the tyme is.
Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
34 For as a man that is gon fer in pilgrimage, lefte his hous, and yaf to his seruauntis power of euery work, and comaundide to the porter, that he wake.
Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35 Therfor wake ye, for ye witen not, whanne the lord of the hous cometh, in the euentide, or at mydnyyt, or at cockis crowyng, or in the mornyng;
To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
36 leste whanne he cometh sodenli, he fynde you slepynge.
Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
37 Forsothe that that Y seie to you, Y seie to alle, Wake ye.
Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”