< Mark 10 >

1 And Jhesus roos vp fro thennus, and cam in to the coostis of Judee ouer Jordan; and eftsoones the puple cam togidere to hym, and as he was wont, eftsoone he tauyte hem.
Yesu ya bar wannan wurin, ya tafi yankin Yahudiya, wajen hayin kogin Urdun. Sai jama'a suka je wurinsa. Ya ci gaba da koya masu, kamar yadda ya zama al'adarsa.
2 And the Farisees camen, and axiden hym, Whether it be leueful to a man to leeue his wijf? and thei temptiden hym.
Sai Farisawa su ka zo wurinsa, su ka ce, '' dai dai ne mutum ya saki matarsa?'' Wannan tambaya sun yi ta ne domin su gwada shi.
3 And he answeride, and seide to hem, What comaundide Moises to you?
Ya amsa ya ce, menene Musa ya umarce ku?
4 And thei seiden, Moises suffride to write a libel of forsaking, and to forsake.
Suka ce, ''Musa ya yarda mutum ya rubuta takardar saki ga matarsa, ya sallameta ta fita.''
5 `To whiche Jhesus answeride, and seide, For the hardnesse of youre herte Moises wroot to you this comaundement.
“Domin taurin zuciyarku ne ya rubuta maku wannan dokar,” Yesu ya ce masu.
6 But fro the bigynnyng of creature God made hem male and female;
Amman tun daga farkon halitta, 'Allah ya halicci namiji da ta mata.'
7 and seide, For this thing a man schal leeue his fadir and modir,
Domin wannan dalilin ne mutum zai rabu mahaifinsa da mahaifiyarsa ya mannewa matarsa.
8 and schal drawe to hys wijf, and thei schulen be tweyne in o flesch. And so now thei ben not tweyne, but o flesch.
Su biyu kuwa sun zama jiki daya, ba biyu ba,
9 Therfor that thing that God ioynede togidere, no man departe.
Saboda haka abinda Allah ya hada kada mutum ya raba.”
10 And eftsoone in the hous hise disciplis axiden hym of the same thing.
Lokacin da suke cikin gida, sai almajiransa suka sake tambayarsa akan wannan magana.
11 And he seide to hem, Who euer leeuith his wijf, and weddith another, he doith auowtri on hir.
Ya ce da su. Dukan wanda ya saki matarsa ya kuma auro wata matar yayi zina da ita kenan.
12 And if the wijf leeue hir housebonde, and be weddid to another man, sche doith letcherie.
Haka nan duk matar da ta saki mijinta ta auri wani ta yi zina da shi kenan.”
13 And thei brouyten to hym litle children, that he schulde touche hem; and the disciplis threteneden the men, that brouyten hem.
Mutane suka kawo masa 'ya'yansu kanana don ya taba su, sai almajiransa suka kwabe su.
14 And whanne Jhesus hadde seyn hem, he baar heuy, and seide to hem, Suffre ye litle children to come to me, and forbede ye hem not, for of suche is the kyngdom of God.
Da Yesu ya gani, ya ji haushi, ya ce masu. Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su domin mulkin Allah na irinsu ne.
15 Treuli Y seie to you, who euer resseyueth not the kyngdom of God as a litil child, he schal not entre in to it.
Gaskiya na ke fada maku duk mutumin da bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, babu shakka ba zai shiga mulkin Allah ba.
16 And he biclippide hem, and leide hise hondis on hem, and blisside hem.
Sai ya rungume su ya sa masu albarka.
17 And whanne Jhesus was gon out in the weie, a man ranne bifore, and knelide bifor hym, and preiede hym, and seide, Good maister, what schal Y do, that Y resseyue euerlastynge lijf? (aiōnios g166)
Lokacin da ya fara tafiya, sai wani mutum ya rugo wurinsa, ya durkusa a gabansa. Ya tambaye shi, yace ya ''Malam managarci, me zan yi domin in sami rai na har abada?'' (aiōnios g166)
18 And Jhesus seide to hym, What seist thou, that Y am good? Ther is no man good, but God hym silf.
Amma Yesu ya ce masa. Don me ka ke kira na managarci? Babu wani managarci sai dai Allah kadai.
19 Thou knowist the comaundementis, do thou noon auowtrie, `sle not, stele not, seie not fals witnessyng, do no fraude, worschipe thi fadir and thi modir.
Kasan dokokin. Kada ka yi kisan kai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar zur, kada ka yi zamba, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
20 And he answeride, and seide to hym, Maister, Y haue kept alle these thingis fro my yongthe.
Sai mutumin ya ce masa Malam ai na kiyayye duk wadannan abubuwa tun ina yaro.
21 And Jhesus bihelde hym, and louede hym, and seide to hym, O thing faileth to thee; go thou, and sille alle thingis that thou hast, and yyue to pore men, and thou schalt haue tresoure in heuene; and come, sue thou me.
Yesu ya dube shi duban kauna ya ce masa. Abu daya ka rasa. Shi ne ka je ka sayar da duk mallakarka ka ba mabukata, za ka sami wadata a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.
22 And he was ful sori in the word, and wente awei mornyng, for he hadde many possessiouns.
Da ya ji haka sai ransa ya baci, ya tafi yana bakin ciki, don shi mai arziki ne kwarai.
23 And Jhesus bihelde aboute, and seide to hise disciplis, Hou hard thei that han ritchessis schulen entre in to the kyngdom of God.
Yesu ya dubi almajiransa ya ce. ''Yana da wuya masu arziki su shiga mulkin Allah!''
24 And the disciplis weren astonyed in hise wordis. And Jhesus eftsoone answeride, and seide `to hem, Ye litle children, hou hard it is for men that tristen in ritchessis to entre in to the kyngdom of God.
Almajiransa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ce masu, ya ku ya'ya'na yana da wuya kamar me a shiga mulkin Allah.
25 It is liyter a camele to passe thorou a nedlis iye, than a riche man to entre in to the kyngdom of God.
Zai zama da sauki ga rakumi yabi ta kafar allura da mai arziki ya shiga mulkin Allah.
26 And thei wondriden more, and seiden among hem silf, And who may be sauyd?
Sai suka cika da mamaki sosai, su kace wa juna, ''to idan haka ne wanene zai iya tsira kenan?''
27 And Jhesus bihelde hem, and seide, Anentis men it is impossible, but not anentis God; for alle thingis ben possible anentis God.
Yesu ya dube su ya ce masu. Ga mutane a bu ne mai wuyar gaske, amma a wurin Allah komai yiwuwa ne.
28 And Petir bigan to seie to hym, Lo! we han left alle thingis, and han sued thee.
Bitrus ya ce masa, ''to gashi mu mun bar kome, mun bika''.
29 Jhesus answeride, and seide, Treuli Y seie to you, ther is no man that leeueth hous, or britheren, or sistris, or fadir, or modir, or children, or feeldis for me and for the gospel,
Yesu ya ce. Gaskiya na ke fada maku, babu wanda zai bar gidansa, da yan'uwansa maza da mata, da mahaifiya ko mahaifi, ko 'ya'ya ko gona, saboda da ni da kuma bishara,
30 which schal not take an hundrid fold so myche now in this tyme, housis, and britheren, and sistris, and modris, and children, and feeldis, with persecuciouns, and in the world to comynge euerlastynge lijf. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa'annan ya rasa samun nikinsu dari a zamanin yanzu, na gidaje, da yan'uwa mata da maza' da iyaye mata da 'ya'ya da gonaki, game da tsanani, a duniya mai zuw kuma ya sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 But many schulen be, the firste the last, and the last the firste.
Da yawa wadanda suke na farko za su koma na karshe, na karshe kuma za su zama na farko.
32 And thei weren in the weie goynge vp to Jerusalem; and Jhesus wente bifor hem, and thei wondriden, and foleweden, and dredden. And eftsoone Jhesus took the twelue, and bigan to seie to hem, what thingis weren to come to hym.
Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na gabansu. Almajiransa sun yi mamaki, mutane da ke biye da su kuwa sun tsorata. Yesu kuwa ya sake kebe sha biyun nan, ya fara fada masu abin da zai same shi.
33 For lo! we stien to Jerusalem, and mannus sone schal be bitraied to the princis of prestis, and to scribis, and to the eldre men; and thei schulen dampne hym bi deth, and thei schulen take hym to hethene men. And thei schulen scorne hym,
“Kun ga, za mu Urushalima za a bada Dan mutum ga manyan Firistoci da malan Attaura, za su kuma yi masa hukuncin kisa su kuma bada shi ga al'ummai.
34 and bispete hym, and bete him; and thei schulen sle hym, and in the thridde dai he schal rise ayen.
Za su yi masa ba a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuwa zai tashi.”
35 And James and Joon, Zebedees sones, camen to hym, and seiden, Maister, we wolen, that what euer we axen, thou do to vs.
Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka zo wurin sa, suka ce, ''Malam muna so kayi mana duk abin da mu ka roke ka''
36 And he seide to hem, What wolen ye that Y do to you?
Ya ce masu. ''Me ku ke so in yi maku?''
37 And thei seiden, Graunte to vs, that we sitten `the toon at thi riythalf, and the tother at thi left half, in thi glorie.
Suka ce, ''ka yardar mana, a ranar daukakarka, mu zauna daya a damanka, daya kuma a hagunka.''
38 And Jhesus seide to hem, Ye witen not what ye axen; moun ye drynke the cuppe, which Y schal drynke, or be waischun with the baptym, in which Y am baptisid?
Yesu ya ce masu. ''Ba ku san abinda ku ke roka ba. Kwa iya sha daga kokon da zan sha? Ko kuma za a yi maku baftismar da za a yi mani?''
39 And thei seiden to hym, We moun. And Jhesus seide to hem, Ye schulen drynke the cuppe that Y drynke, and ye schulen be waschun with the baptym, in which Y am baptisid;
Suka fada masa, ''Zamu iya.'' Yesu ya ce masu, '' kokon da zan sha, da shi zaku sha, baftismar da za ayi mani kuma da ita za a yi maku.''
40 but to sitte at my riythalf or lefthalf is not myn to yyue to you, but to whiche it is maad redi.
Amma zama a damata, ko a haguna, ba na wa ba ne da zan bayar, ai na wadanda a ka shiryawa ne.”
41 And the ten herden, and bigunnen to haue indignacioun of James and Joon.
Da sauran almajiran nan goma suka ji, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya.
42 But Jhesus clepide hem, and seide to hem, Ye witen, that thei that semen to haue prynshode of folkis, ben lordis of hem, and the princes of hem han power of hem.
Yesu kuma ya kira su wurinsa ya ce masu, '' kun sani wadanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna masu iko, hakimansu kuma sukan gasa masu iko.
43 But it is not so among you, but who euer wole be maad gretter, schal be youre mynyster;
Amma ba haka zai kasance a tsakaninku ba. Duk wanda ya ke son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.
44 and who euer wole be the firste among you, schal be seruaunt of alle.
Duk wanda ya ke so ya shugabance ku lalle ne ya zama bawan kowa.
45 For whi mannus sone cam not, that it schulde be mynystrid to hym, but that he schulde mynystre, and yyue his lijf ayenbiyng for manye.
Saboda haka ne Dan mutum ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi yayi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda da mutane da yawa.”
46 And thei camen to Jerico; and whanne he yede forth fro Jerico, and hise disciplis, and a ful myche puple, Barthymeus, a blynde man, the sone of Thimei, sat bisidis the weie, and beggide.
Sa'adda suka iso Yariko, yana fita daga Yariko kenan, shi da almajiransa, da wani babban taro, sai ga wani makaho mai bara, mai suna Bartimawas dan Timawas yana zaune a gefen hanya.
47 And whanne he herde, that it is Jhesus of Nazareth, he bigan to crie, and seie, Jhesu, the sone of Dauid, haue merci on me.
Da ya ji Yesu Banazare ne, ya fara daga murya yana cewa, ''Ya Yesu, Dan Dauda, kaji tausayina''
48 And manye thretneden hym, that he schulde be stille; and he criede myche the more, Jhesu, the sone of Dauid, haue merci on me.
Mutane da yawa suka kwabe shi, cewa yayi shiru. Sai ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, Ya Dan Dauda ka yi mani jinkai, ka ji tausayina!”
49 And Jhesus stood, and comaundide hym to be clepid; and thei clepen the blynde man, and seien to hym, Be thou of betere herte, rise vp, he clepith thee.
Yesu ya tsaya ya ce, ku kirawo shi. Su kuwa suka kirawo makahon suka ce masa. ''Albishrinka, ta so! Yana kiranka.''
50 And he castide awei his cloth, and skippide, and cam to hym.
Makahon ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.
51 And Jhesus answeride, and seide to hym, What wolt thou, that Y schal do to thee? The blynde man seide to hym, Maister, that Y se.
Yesu ya tambaye shi, ya ce, '' me ka ke so in yi maka?'' Makahon ya ce, ''Malam in sami gani.''
52 Jhesus seide to hym, Go thou, thi feith hath maad thee saaf. And anoon he saye, and suede hym in the weie.
Yesu ya ce masa. ''Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.'' Nan take idanunsa suka bude, ya bi Yesu, suka tafi tare.

< Mark 10 >