< Mark 1 >

1 The bigynnyng of the gospel of Jhesu Crist, the sone of God.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 As it is writun in Ysaie, the prophete, Lo! Y sende myn aungel bifor thi face, that schal make thi weie redi bifor thee.
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 The vois of a crier in desert, Make ye redi the weie of the Lord, make ye hise paththis riyt.
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 Joon was in desert baptisynge, and prechynge the baptym of penaunce, in to remissioun of synnes.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 And al the cuntre of Judee wente out to hym, and alle men of Jerusalem; and thei weren baptisid of hym in the flom Jordan, `and knoulechiden her synnes.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 And Joon was clothid with heeris of camels, and a girdil of skyn was about hise leendis; and he ete hony soukis, and wilde hony, and prechide,
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 and seide, A stronger than Y schal come aftir me, and Y am not worthi to knele doun, and vnlace his schoone.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 Y haue baptisid you in watir; but he schal baptise you in the Hooli Goost.
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 And it was don in tho daies, Jhesus cam fro Nazareth of Galilee, and was baptisid of Joon in Jordan.
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 And anoon he wente up of the watir, and saye heuenes opened, and the Hooli Goost comynge doun as a culuer, and dwellynge in hym.
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 And a vois was maad fro heuenes, Thou art my loued sone, in thee Y am plesid.
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 And anoon the Spirit puttide hym forth in to deseert.
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 And he was in deseert fourti daies and fourti nyytis, and was temptid of Sathanas, and he was with beestis, and aungels mynystriden to hym.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 But aftir that Joon was takun, Jhesus cam in to Galilee, and prechide the gospel of the kyngdoom of God,
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 and seide, That the tyme is fulfillid, and the kyngdoom of God schal come nyy; do ye penaunce, and bileue ye to the gospel.
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 And as he passide bisidis the see of Galilee, he say Symount, and Andrew, his brother, castynge her nettis in to the see; for thei weren fisscheris.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 And Jhesus seide to hem, Come ye aftir me; Y schal make you to be maad fisscheris of men.
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 And anoon thei leften the nettis, and sueden hym.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 And he yede forth fro thennus a litil, and siy James of Zebedee, and Joon, his brother, in a boot makynge nettis.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 And anoon he clepide hem; and thei leften Zebedee, her fadir, in the boot with hiryd seruauntis, and thei suweden hym.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 And thei entriden in to Capharnaum, and anoon in the sabatys he yede in to a synagoge, and tauyte hem.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 And thei wondriden on his teching; for he tauyte hem, as he that hadde power, and not as scribis.
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 And in the synagoge of hem was a man in an vnclene spirit, and he criede out,
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 and seide, What to vs and to thee, thou Jhesu of Nazareth? hast thou come to distrie vs? Y woot that thou art the hooli of God.
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 And Jhesus thretenede hym, and seide, Wex doumbe, and go out of the man.
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 And the vnclene spirit debreidynge hym, and criynge with greet vois, wente out fro hym.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 And alle men wondriden, so that thei souyten with ynne hem silf, and seiden, What thing is this? what newe doctrine is this? for in power he comaundith to vnclene spiritis, and thei obeyen to hym.
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 And the fame of hym wente forth anoon in to al the cuntree of Galilee.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 And anoon thei yeden out of the synagoge, and camen into the hous of Symount and of Andrewe, with James and Joon.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 And the modir of Symountis wijf lay sijk in fyueris; and anoon thei seien to hym of hyr.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 And he cam nyy, and areride hir, and whanne he hadde take hir hoond, anoon the feuer lefte hir, and sche seruede hem.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 But whanne the euentid was come, and the sonne was gon doun, thei brouyten to hym alle that weren of male ese, and hem that hadden fendis.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 And al the citee was gaderid at the yate.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 And he heelide many, that hadden dyuerse sijknessis, and he castide out many feendis, and he suffride hem not to speke, for thei knewen hym.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 And he roos ful eerli, and yede out, and wente in to a desert place, and preiede there.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 And Symount suede hym, and thei that weren with hym.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 And whanne thei hadden founde hym, thei seiden to hym, That alle men seken thee.
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 And he seide to hem, Go we in to the next townes and citees, that Y preche also there, for her to Y cam.
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 And he prechide in the synagogis of hem, and in al Galilee, and castide out feendis.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 And a leprouse man cam to hym, and bisouyte, `and knelide, and seide, If thou wolt, thou maist clense me.
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 And Jhesus hadde mercy on hym, and streiyte out his hoond, and towchyde hym, and seide to hym, I wole, be thou maad cleene.
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 And whanne he hadde seide this, anoon the lepre partyde awey fro hym, and he was clensyd.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 And Jhesus thretenede hym, and anoon Jhesus putte hym out,
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 and seyde to hym, Se thou, seye to no man; but go, schewe thee to the pryncys of prestys, and offre for thi clensynge in to wytnessyng to hem, tho thingis that Moyses bad.
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 And he yede out, and bigan to preche, and publische the word, so that now he myyte not go opynli in to the citee, but be withoutforth in desert placis; and thei camen to hym on alle sidis.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< Mark 1 >