< Luke 9 >

1 And whanne the twelue apostlis weren clepid togidir, Jhesus yaf to hem vertu and power on alle deuelis, and that thei schulden heele sijknessis.
Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
2 And he sente hem for to preche the kyngdom of God, and to heele sijk men.
Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 And he seide to hem, No thing take ye in the weie, nether yerde, ne scrippe, nether breed, ne money, and nether haue ye two cootis.
Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
4 And in to what hous that ye entren, dwelle ye there, and go ye not out fro thennus.
Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
5 And who euer resseyuen not you, go ye out of that citee, and schake ye of the poudir of youre feet in to witnessyng on hem.
In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
6 And thei yeden forth, and wenten aboute bi castels, prechynge and helynge euery where.
Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
7 And Eroude tetrak herde alle thingis that weren don of hym, and he doutide,
Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
8 for that it was seide of sum men, that Joon was risen fro deth; and of summen, that Elie hadde apperid; but of othere, that oon of the elde prophetis was risun.
waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
9 And Eroude seide, Y haue biheedid Joon; and who is this, of whom Y here siche thingis? And he souyte to se hym.
Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
10 And the apostlis turneden ayen, and tolden to hym alle thingis that thei hadden don. And he took hem, and wente bisidis in to a desert place, that is Bethsada.
Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
11 And whanne the puple knewen this, thei folewiden hym. And he resseyuede hem, and spak to hem of the kyngdom of God; and he heelide hem that hadden neede of cure.
Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
12 And the dai bigan to bowe doun, and the twelue camen, and seiden to hym, Leeue the puple, that thei go, and turne in to castels and townes, that ben aboute, that thei fynde mete, for we ben here in a desert place.
Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
13 And he seide to hem, Yue ye to hem to ete. And thei seiden, Ther ben not to vs mo than fyue looues and twei fischis, but perauenture that we go, and bie meetis to al this puple.
Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
14 And the men weren almost fyue thousynde. And he seide to hise disciplis, Make ye hem sitte to mete bi cumpanyes, a fifti to gidir.
Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
15 And thei diden so, and thei maden alle men sitte to mete.
Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
16 And whanne he hadde take the fyue looues and twei fischis, he biheeld in to heuene, and blesside hem, and brak, and delide to hise disciplis, that thei schulden sette forth bifor the cumpanyes.
Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
17 And alle men eeten, and weren fulfillid; and that that lefte to hem of brokun metis was takun vp, twelue cofyns.
Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
18 And it was don, whanne he was aloone preiynge, hise disciplis weren with hym, and he axide hem, and seide, Whom seien the puple that Y am?
Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
19 And thei answeriden, and seiden, Joon Baptist, othir seien Elie, and othir seien, o profete of the formere is risun.
Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
20 And he seide to hem, But who seien ye that Y am? Symount Petir answeride, and seide, The Crist of God.
“Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
21 And he blamynge hem comaundide that thei schulden seie to no man,
Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
22 and seide these thingis, For it bihoueth mannus sone to suffre many thingis, and to be repreued of the elder men, and of the princis of prestis, and of scribis, and to be slayn, and the thridde dai to rise ayen.
Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
23 And he seide to alle, If ony wole come aftir me, denye he hym silf, and take he his cross euery dai, and sue he me.
Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
24 For he that wole make his lijf saaf schal leese it; and he that leesith his lijf for me, schal make it saaf.
Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
25 And what profitith it to a man, if he wynne al the world, and leese hymsilf, and do peiryng of him silf.
Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
26 For who so schameth me and my wordis, mannus sone schal schame hym, whanne he cometh in his maieste, and of the fadris, and of the hooli aungels.
Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
27 And Y seie to you, verily ther ben summe stondynge here, whiche schulen not taste deeth, til thei seen the rewme of God.
“Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
28 And it was don aftir these wordis almest eiyte daies, and he took Petre and James and Joon, and he stiede in to an hil, to preye.
Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
29 And while he preiede, the licnesse of his cheer was chaungid, and his clothing was whit schynynge.
Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
30 And lo! two men spaken with hym,
Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
31 and Moises and Helie weren seen in maieste; and thei sayn his goyng out, which he schulde fulfille in Jerusalem.
Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
32 And Petre, and thei that weren with hym, weren heuy of sleep, and thei wakynge saien his majeste, and the twey men that stoden with hym.
Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
33 And it was don, whanne thei departiden fro hym, Petir seide to Jhesu, Comaundour, it is good that we be here, and make we here thre tabernaclis, oon to thee, and oon to Moises, and oon to Elie. And he wiste not what he schulde seie.
Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
34 But while he spak these thingis, a cloude was maad, and ouerschadewide hem; and thei dredden, whanne thei entriden in to the cloude.
Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
35 And a vois was maad out of the cloude, and seide, This is my derworth sone, here ye hym.
Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
36 And while the vois was maad, Jhesu was foundun aloone. And thei weren stille, and to no man seiden in tho daies ouyt of tho thingis, that thei hadden seyn.
Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
37 But it was doon in the dai suynge, whanne thei camen doun of the hil, myche puple mette hem.
Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
38 And lo! a man of the cumpany criede, and seide, Maister, Y biseche thee, biholde my sone, for Y haue no mo; and lo!
Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
39 a spirit takith hym, and sudenli he crieth, and hurtlith doun, and to-drawith hym with fome, and vnneth he goith awei al to-drawynge hym.
Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
40 And Y preiede thi disciplis, that thei schulden caste hym out, and thei myyten not.
Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
41 And Jhesus answerde and seide to hem, A! vnfeithful generacioun and weiward, hou long schal Y be at you, and suffre you? brynge hidur thi sone.
Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
42 And whanne he cam nyy, the deuel hurtlide hym doun, and to-braidide hym. And Jhesus blamyde `the vnclene spirit, and heelide the child, and yeldide him to his fadir.
Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
43 And alle men wondriden greetli in the gretnesse of God. And whanne alle men wondriden in alle thingis that he dide, he seide to hise disciplis,
Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
44 Putte ye these wordis in youre hertis, for it is to come, that mannus sone be bitrayed in to the hondis of men.
“Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
45 And thei knewen not this word, and it was hid bifor hem, that thei feeliden it not; and thei dredden to axe hym of this word.
Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
46 But a thouyt entride in to hem, who of hem schulde be grettest.
Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
47 And Jhesu, seynge the thouytis of the herte of hem, took a child, and settide hym bisidis hym;
Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
48 and seide to hem, Who euer resseyueth this child in my name, resseyueth me; and who euer resseyueth me, resseiueth him that sente me; for he that is leest among you alle, is the grettest.
Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
49 And Joon answeride and seide, Comaundoure, we sayn a man castynge out feendis in thi name, and we han forbedun hym, for he sueth not thee with vs.
Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
50 And Jhesus seide to hym, Nyle ye forbede, for he that is not ayens vs, is for vs.
Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
51 And it was don, whanne the daies of his takyng vp weren fulfillid, he settide faste his face, to go to Jerusalem,
Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
52 and sente messangeris bifor his siyt. And thei yeden, and entriden in to a citee of Samaritans, to make redi to hym.
Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
53 And thei resseyueden not hym, for the face `was of hym goynge in to Jerusalem.
Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
54 And whanne James and Joon, hise disciplis, seyn, thei seiden, Lord, wolt thou that we seien, that fier come doun fro heuene, and waste hem?
Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
55 And he turnede, and blamyde hem, and seide, Ye witen not, whos spiritis ye ben;
Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
56 for mannus sone cam not to leese mennus soulis, but to saue. And thei wenten in to another castel.
Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
57 And it was don, whanne thei walkeden in the weie, a man seide to hym, Y schal sue thee, whidur euer thou go.
Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
58 And Jhesus seide to hym, Foxis han dennes, and briddis of the eir han nestis, but mannus sone hath not where he reste his heed.
Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
59 And he seide to another, Sue thou me. And he seide, Lord, suffre me first to go, and birie my fadir.
Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
60 And Jhesus seide to hym, Suffre that deede men birie hir deede men; but go thou, and telle the kyngdom of God.
Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
61 And another seide, Lord, Y schal sue thee, but first suffre me to leeue `alle thingis that ben at hoom.
Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
62 And Jhesus seide to hym, No man that puttith his hoond to the plouy, and biholdynge bacward, is able to the rewme of God.
Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”

< Luke 9 >