< Luke 1 >
1 Forsothe for manye men enforceden to ordeyne the tellyng of thingis, whiche ben fillid in vs,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 as thei that seyn atte the bigynnyng, and weren ministris of the word,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 bitaken, it is seen also to me, hauynge alle thingis diligentli bi ordre, to write to thee,
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 thou best Theofile, that thou knowe the treuthe of tho wordis, of whiche thou art lerned.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 In the daies of Eroude, kyng of Judee, ther was a prest, Sakarie bi name, of the sorte of Abia, and his wijf was of the douytris of Aaron, and hir name was Elizabeth.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 And bothe weren iust bifor God, goynge in alle the maundementis and iustifiyngis of the Lord, withouten pleynt.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 And thei hadden no child, for Elizabeth was bareyn, and bothe weren of grete age in her daies.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 And it bifel, that whanne Zacarie schulde do the office of preesthod, in the ordre of his cours tofor God,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 aftir the custome of the preesthod, he wente forth bi lot, and entride in to the temple, to encense.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 And al the multitude of the puple was with outforth, and preiede in the our of encensyng.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 And an aungel of the Lord apperide to hym, and stood on the riythalf of the auter of encense.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 And Zacarie seynge was afraied, and drede fel vpon hym.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 And the aungel seide to hym, Zacarie, drede thou not; for thi preyer is herd, and Elizabeth, thi wijf, schal bere to thee a sone, and his name schal be clepid Joon.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 And ioye and gladyng schal be to thee; and many schulen `haue ioye in his natyuyte.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 For he schal be greet bifor the Lord, and he schal not drynke wyn and sidir, and he schal be fulfillid with the Hooli Goost yit of his modir wombe.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 And he schal conuerte many of the children of Israel to her Lord God;
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 and he schal go bifor hym in the spirit and the vertu of Helie; and he schal turne the hertis of the fadris in to the sones, and men out of bileue to the prudence of iust men, to make redi a perfit puple to the Lord.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 And Zacarie seide to the aungel, Wherof schal Y wite this? for Y am eld, and my wijf hath gon fer in to hir daies.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 And the aungel answeride, and seide to hym, For Y am Gabriel, that stonde niy bifor God; and Y am sent to thee to speke, and to euangelize to thee these thingis.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 And lo! thou schalt be doumbe, and thou schalt not mow speke til in to the dai, in which these thingis schulen be don; for thou hast not bileued to my wordis, whiche schulen be fulfillid in her tyme.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 And the puple was abidynge Zacarie, and thei wondriden, that he tariede in the temple.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 And he yede out, and myyte not speke to hem, and thei knewen that he hadde seyn a visioun in the temple. And he bikenyde to hem, and he dwellide stille doumbe.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 And it was don, whanne the daies of his office weren fulfillid, he wente in to his hous.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 And aftir these daies Elizabeth, his wijf, conseyuede, and hidde hir fyue monethis, and seide,
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 For so the Lord dide to me in the daies, in whiche he bihelde, to take awei my repreef among men.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 But in the sixte moneth the aungel Gabriel was sent fro God in to a citee of Galilee, whos name was Nazareth,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 to a maidyn, weddid to a man, whos name was Joseph, of the hous of Dauid; and the name of the maidun was Marie.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 And the aungel entride to hir, and seide, Heil, ful of grace; the Lord be with thee; blessid be thou among wymmen.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 And whanne sche hadde herd, sche was troublid in his word, and thouyte what maner salutacioun this was.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 And the aungel seide to hir, Ne drede thou not, Marie, for thou hast foundun grace anentis God.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 Lo! thou schalt conceyue in wombe, and schalt bere a sone, and thou schalt clepe his name Jhesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 This schal be greet, and he schal be clepid the sone of the Hiyeste; and the Lord God schal yeue to hym the seete of Dauid, his fadir,
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 and he schal regne in the hous of Jacob with outen ende, and of his rewme schal be noon ende. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 And Marie seide to the aungel, On what maner schal this thing be doon, for Y knowe not man?
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 And the aungel answeride, and seide to hir, The Hooly Goost schal come fro aboue in to thee, and the vertu of the Hiyeste schal ouerschadewe thee; and therfor that hooli thing that schal be borun of thee, schal be clepid the sone of God.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 And lo! Elizabeth, thi cosyn, and sche also hath conceyued a sone in hir eelde, and this moneth is the sixte to hir that is clepid bareyn;
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 for euery word schal not be inpossible anentis God.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 And Marie seide, Lo! the handmaydyn of the Lord; be it don to me aftir thi word. And the aungel departide fro hir.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 And Marie roos vp in tho daies, and wente with haaste in to the mounteyns, in to a citee of Judee.
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 And sche entride in to the hous of Zacarie, and grette Elizabeth.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 And it was don, as Elizabeth herde the salutacioun of Marie, the yong child in hir wombe gladide. And Elizabeth was fulfillid with the Hooli Goost,
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 and criede with a greet vois, and seide, Blessid be thou among wymmen, and blessid be the fruyt of thi wombe.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 And whereof is this thing to me, that the modir of my Lord come to me?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 For lo! as the voice of thi salutacioun was maad in myn eeris, the yong child gladide in ioye in my wombe.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 And blessid be thou, that hast bileued, for thilke thingis that ben seid of the Lord to thee, schulen be parfitli don.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 And Marie seide, Mi soule magnyfieth the Lord,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 and my spirit hath gladid in God, myn helthe.
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 For he hath biholdun the mekenesse of his handmaidun.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 For lo! of this alle generaciouns schulen seie that Y am blessid. For he that is myyti hath don to me grete thingis, and his name is hooli.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is fro kynrede in to kynredes, to men that dreden hym.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 He made myyt in his arme, he scaterede proude men with the thouyte of his herte.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 He sette doun myyti men fro sete, and enhaunside meke men.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 He hath fulfillid hungri men with goodis, and he hath left riche men voide.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 He, hauynge mynde of his mercy, took Israel, his child;
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 as he hath spokun to oure fadris, to Abraham and to his seed, in to worldis. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 And Marie dwellide with hir, as it were thre monethis, and turnede ayen in to hir hous.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 But the tyme of beryng child was fulfillid to Elizabeth, and sche bare a sone.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 And the neiyboris and cosyns of hir herden, that the Lord hadde magnyfied his mercy with hir; and thei thankiden hym.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 And it was don in the eiyte dai, thei camen to circumcide the child; and thei clepiden hym Zacarie, bi the name of his fadir.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 And his moder answeride, and seide, Nay, but he schal be clepid Joon.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 And thei seiden to hir, For no man is in thi kynrede, that is clepid this name.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 And thei bikeneden to his fadir, what he wolde that he were clepid.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 And he axynge a poyntil, wroot, seiynge, Joon is his name.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 And alle men wondriden. And anoon his mouth was openyd, and his tunge, and he spak, and blesside God.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 And drede was maad on alle her neiyboris, and alle these wordis weren pupplischid on alle the mounteyns of Judee.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 And alle men that herden puttiden in her herte, and seiden, What maner child schal this be? For the hoond of the Lord was with hym.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 And Zacarie, his fadir, was fulfillid with the Hooli Goost, and prophesiede,
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 and seide, Blessid be the Lord God of Israel, for he hath visitid, and maad redempcioun of his puple.
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 And he hath rerid to vs an horn of heelthe in the hous of Dauid, his child.
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 As he spak bi the mouth of hise hooli prophetis, that weren fro the world. (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 Helthe fro oure enemyes, and fro the hoond of alle men that hatiden vs.
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 To do merci with oure fadris, and to haue mynde of his hooli testament.
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The greet ooth that he swoor to Abraham, oure fadir, to yyue hym silf to vs.
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 That we with out drede delyuered fro the hoond of oure enemyes,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 serue to hym, in hoolynesse and riytwisnesse bifor hym in alle oure daies.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 And thou, child, schalt be clepid the prophete of the Hiyest; for thou schalt go bifor the face of the Lord, to make redi hise weies.
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 To yyue scyence of helthe to his puple, in to remyssioun of her synnes;
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 bi the inwardnesse of the merci of oure God, in the whiche he spryngynge vp fro an hiy hath visitid vs.
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 To yyue liyt to hem that sitten in derknessis and in schadewe of deeth; to dresse oure feet in to the weie of pees.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 And the child wexide, and was coumfortid in spirit, and was in desert placis `til to the dai of his schewing to Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.