< Leviticus 24 >
1 And the Lord spak to Moises, and seide, Comaunde thou to the sones of Israel,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 that thei brynge to thee oile of olyues, pureste oile, and briyt, to the lanternes to be ordeyned contynueli with out the veil of witnessyng,
“Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
3 in the tabernacle of boond of pees; and Aaron schal araye tho lanternes fro euentid `til to euentid bifor the Lord, bi religioun and custom euerlastynge in youre generaciouns;
Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
4 tho schulen be set euere on a clenneste candilstike in the siyt of the Lord.
Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
5 Also thou schalt take wheete flour, and thou schalt bake therof twelue looues, which schulen haue ech bi hem silf twei tenthe partis,
“Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
6 of whiche thou schalt sette sexe on euer eithir side, on a clenneste boord bifor the Lord;
A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
7 and thou schalt sette clereste encense on tho looues, that the looues be in to mynde of offryng of the Lord;
Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
8 bi ech sabat tho schulen be chaungid bifor the Lord, and schulen be takun of the sones of Israel bi euerlastynge boond of pees;
Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
9 and tho schulen be Aarons and hise sones, that thei ete tho in the hooli place, for it is hooli of the noumbre of hooli thingis, of the sacrifices of the Lord, bi euerlastynge lawe.
Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
10 Lo! forsothe the sone of a womman of Israel, whom sche childide of a man Egipcian, yede out among the sones of Israel, and chidde in the castels with a man of Israel,
To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
11 and whanne he hadde blasfemyd the name of the Lord, and hadde cursid the Lord, he was brouyt to Moises; forsothe his modir was clepid Salumyth, the douytir of Dabry, of the lynage of Dan;
Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 and thei senten hym to prisoun, til thei wisten what the Lord comaundide.
Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
13 And the Lord spak to Moises and seide,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
14 Lede out the blasfemere without the castels, and alle men that herden, sette her hondis on his heed, and al the puple stone hym.
“Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
15 And thou schalt speke to the sones of Israel, A man that cursith his God,
Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
16 schal bere his synne, and he that blasfemeth the name of the Lord, die bi deeth; al the multitude of the puple schal oppresse hym with stoonus, whether he that blasfemede the name of the Lord is a citeseyn, whether a pilgrym, die he bi deeth.
duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
17 He that smytith and sleeth a man, die bi deeth;
“‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18 he that smytith a beeste, yelde oon in his stide, that is, lijf for lijf.
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19 If a man yyueth a wem to ony of hise citeseyns, as he dide, so be it don to him;
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20 he schal restore brekyng for brekyng, iye for iye, tooth for tooth; what maner wem he yaf, he schal be compellid to suffre sich a wem.
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21 He that smytith werk beeste, yeelde another; he that smytith a man, schal be punyschid.
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
22 Euene doom be among you, whether a pilgrym ethir a citeseyn synneth, for Y am youre Lord God.
Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 And Moyses spak to the sones of Israel, and thei brouyten forth out of the castels hym that blasfemede, and oppressiden with stoonus. And the sones of Israel diden, as the Lord comaundide to Moyses.
Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.