< Leviticus 22 >
1 And the Lord spak to Moises, and seide, Speke thou to Aaron and to hise sones,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 that thei be war of these thingis of the sones of Israel, whiche thingis ben halewid; and that they defoule not the name of thingis halewid to me, whiche thingis thei offren; Y am the Lord.
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
3 Seie thou to hem, and to the aftir comeris of hem, Ech man of youre kynrede, `which man neiyeth to tho thingis that ben halewid, and whiche thingis the sones of Israel offreden to the Lord, in `which man is vnclennesse, schal perische bifor the Lord; Y am the Lord.
“Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
4 A man of the seed of Aaron, `which man is leprouse, ethir suffrith `fletyng out of seed, schal not ete of these thingis, that ben halewid to me, til he be heelid. He that touchith an vncleene thing on a deed bodi, and fro whom the seed as of leccherie goith out, and which touchith a crepynge beeste,
“‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
5 and what euer vncleene thing, whos touchyng is foul,
da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
6 schal be vncleene `til to euentid, and he schal not ete these thingis, that ben halewid to me; but whanne he hath waische his fleisch in watir,
duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
7 and the sunne hath go doun, thanne he schal be clensid, and schal ete halewid thingis, for it is his mete.
Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
8 He schal not ete a thing deed bi it silf, and takun of a beeste, nethir he schal be defoulid in tho; Y am the Lord.
Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
9 Thei schulen kepe myn heestis, that thei be not suget to synne, and die in the seyntuarye, whanne thei han defoulid it; Y am the Lord that halewe you.
“‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
10 Ech alien schal not ete of thingis halewid; the hyne which is a straunger, and the hirid man of the preest, schulen not ete of tho. Sotheli these seruauntis,
“‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
11 whom the preest hath bouyt, and which is a borun seruaunt of his hows, schulen ete of tho.
Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
12 If the `douyter of the preest is weddid to ony of the puple, sche schal not ete of these thingis that ben halewid, and of the firste fruytis;
In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
13 sotheli if sche is a widewe, ether forsakun, and turneth ayen with out fre children to `the hows of hir fadir, sche schal be susteyned bi the metis of hir fadir, as a damysel was wont; ech alien hath not power to ete of tho.
Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
14 He that etith bi ignoraunce of halewid thingis, schal adde the fyuethe part with that that he eet, and `schal yyue to the preest in seyntuarie,
“‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
15 and thei schulen not defoule the halewid thingis of the sones of Israel, whiche thei offren to the Lord,
Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
16 lest perauenture thei suffren the wickidnesse of her trespas, whanne thei han ete halewid thingis; Y am the Lord that `halewe hem.
ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
17 The Lord spak to Moises, and seide,
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Speke thou to Aaron and to hise sones, and to alle the sones of Israel, and thou schalt seie to hem, A man of the hous of Israel and of comelyngis that dwellen at hem, which offrith his offryng to the Lord, and ethir paieth avowis, ethir offrith bi his fre wille, what euer thing he offrith in to brent sacrifice of the Lord, that it be offrid bi you,
“Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
19 it schal be a male without wem, of oxen, and of scheep, and of geet; if it hath a wem,
dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
20 ye schulen not offre, nether it schal be acceptable.
Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
21 A man that offrith a sacrifice of pesyble thingis to the Lord, and ethir paieth auowis, ethir offrith bi fre wille, as wel of oxun as of scheep, he schal offre a beeste without wem, that it be acceptable; ech wem schal not be ther ynne.
Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
22 If it is blynd, if it is brokun, if it hath a scar, if it hath whelkis, ether scabbe, ethir drie scabbe, ye schulen not offre tho beestis to the Lord, nether ye schulen brenne of tho beestis on the auter of the Lord.
Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
23 A man may offre wilfuli an oxe and scheep, whanne the eere and tail ben kit of; but avow may not be paied of these beestis.
Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
24 Ye schulen not offre to the Lord ony beeste, whose priuy membris ben brokun, ethir brisid, ether kit, and takun awey, and outerli ye schulen not do these thingis in youre lond.
Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
25 Of `the hond of an alien ye schulen not offre looues to youre God, and what euer other thing he wole yyue, for alle thingis ben corrupt and defoulid; ye schulen not resseyue tho.
Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
26 And the Lord spak to Moises,
Ubangiji ya ce wa Musa,
27 and seide, Whanne an oxe, scheep and goet ben brouyt forth `of the modris wombe, in seuene daies tho schulen be vnder `the tete of her modir; sotheli in the eiyte dai, and fro thennus forth, tho moun be offrid to the Lord,
“Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
28 whether thilke is a cow, whether `thilke is a scheep; tho schulen not be offrid in o dai with her fruytis.
Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
29 If ye offren to the Lord a sacrifice for the doyng of thankyngis, that it mai be plesaunt,
“Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
30 ye schulen ete it in the same dai in which it is offrid; ony thing schal not leeue in the morewtid of the tother dai; Y am the Lord.
Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
31 Kepe ye myn heestis, and do ye tho; Y am the Lord.
“Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
32 Defoule ye not myn hooli name, that Y be halewid in the myddis of the sones of Israel; Y am the Lord, that halewe you, and ledde you out of the lond of Egipt,
Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
33 that Y schulde be to you in to God; Y am the Lord.
da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”