< Judges 8 >

1 And the men of Effraym seiden to hym, What is this thing, which thou woldist do, that thou clepidist not vs, whanne thou yedist to batel ayens Madian? And thei chidden strongli, and almest diden violence.
To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
2 To whiche he answeride, `What sotheli siche thing myyte Y do, what maner thing ye diden? Whethir a reisyn of Effraym is not betere than the vindagis of Abiezer?
Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
3 And the Lord bitook in to youre hondis the princes of Madian, Oreb and Zeb. What sich thing myyte Y do, what maner thing ye diden? And whanne he hadde spoke this thing, the spirit of hem restide, bi which thei bolneden ayens hym.
Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
4 And whanne Gedeon hadde come to Jordan, he passide it with thre hundrid men, that weren with hym; and for weerynesse thei myyten not pursue hem that fledden.
Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
5 And he seide to the men of Socoth, Y biseche, yyue ye looues to the puple, which is with me; for thei failiden greetli, that we moun pursue Zebee and Salmana, kyngis of Madian.
Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
6 The princes of Socoth answeriden in scorne, In hap the pawmes of the hondis of Zebee and of Salmana ben in thin hond, and therfor thou axist, that we yyue looues to thin oost.
Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
7 To whiche he seide, Therfor, whanne the Lord schal bitake Zebee and Salmana in to myn hondis, and whanne Y schal turne ayen ouercomere in pees, Y schal to-reende youre fleischis with the thornes and breris of deseert.
Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
8 And he stiede fro thennus, and cam in to Phanuel; and he spak lijk thingis to men of that place, to whom also thei answeriden, as the men of Socoth hadden answerid.
Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
9 And so he seide to hem, Whanne Y schal turne ayen ouercomere in pees, Y schal distrie this tour.
Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
10 Forsothe Zebee and Salmana restiden with al her oost; for fiftene thousynde men leften of alle the cumpenyes of the `puplis of the eest, whanne an hundrid and twenti thousynde of `fiyteris and of men drawynge out swerd weren slayn.
To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
11 And Gedeon stiede bi the weye of hem that dwelliden in tabernaclis at the eest coost of Nobe and of Lethoa, and smoot the `tentis of enemyes, that weren sikur, and supposiden not ony thing of aduersite.
Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
12 And Zebee and Salmana fledden, whiche Gedeon pursuede and took, whanne al `the oost of hem was disturblid.
Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
13 And he turnede ayen fro batel bifor the `risyng of the sunne,
Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
14 and took a child of the men of Socoth; and he axide hym the names of the princes and eldere men of Socoth; and he descryuede seuene and seuenti men in noumbre.
Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
15 And he cam to Socoth, and seide to hem, Lo Zebee and Salmana! of whiche ye vpbreideden me, and seiden, In hap the hondis of Zebee and of Salmana ben in thin hondis, and therfor thou axist, that we yyue looues to men, that ben weeri and failiden.
Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
16 Therfor Gedeon took the eldere men of the citee, and thornes and breris of deseert, and he to-rente with tho, and al to-brak the men of Socoth; also he destriede the tour of Phanuel,
Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
17 whanne the dwelleris of the citee weren slayn.
Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
18 And he seide to Zebee and Salmana, What maner men weren thei, whiche ye killiden in Thabor? Whiche answeriden, Thei weren lijk thee, and oon of hem was as the sone of a kyng.
Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
19 To whiche he seide, Thei weren my britheren, the sones of my modir; the Lord lyueth, if ye hadden saued hem, Y `nolde sle you.
Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
20 And he seide to Jepther, his firste gendrid sone, Rise thou, and sle hem. Which drow not swerd; for he dredde, for he was yit a child.
Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
21 And Zebee and Salmana seiden, Ryse thou, and falle on vs; for thou art bi the age and strengthe of man. Gedeon roos, and killide Zebee and Salmana, and took the ournementis, and bellis, with whiche the neckis of kyngis camels ben wont to be maad fair.
Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
22 And alle the men of Israel seiden to Gedeon, Be thou lord of vs, thou, and thi sone, and the sone of thi sone; for thou deliueridist vs fro the hond of Madian.
Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
23 To whiche he seide, Y schal not be lord of you, nethir my sone schal be lord on you, but the Lord schal be lord.
Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
24 And he seide to hem, Y axe oon axyng of you, yyue ye to me the eere ryngis of youre prey; for Ismaelitis weren wont to haue goldun eere ryngis.
Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
25 Whiche answeriden, We schulen yyue moost gladli. And thei spredden forth a mentil on the erthe, and castiden forth therynne `eere ryngis of the prey;
Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
26 and the weiyte of `eere ryngis axid was a thousynde and seuene hundrid siclis of gold, with out ournementis and brochis and cloth of purpur, whiche the kyngis of Madian weren wont to vse, and outakun goldun bies of camels.
Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
27 And Gedeon made therof ephot, that is, a preestis cloth, `and propir cloth of the hiyeste preest, and he puttide it in his citee Ephra; and al Israel diden fornycacioun, `that is ydolatrye, ther ynne; and it was maad to Gedeon and to al his hows in to fallyng.
Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
28 Forsothe Madian was maad low bifor the sones of Israel, and thei myyten no more reise nollis; but the lond restide fourti yeer, in whiche Gedeon was souereyn.
Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
29 And so Jerobaal, sone of Joas, yede, and dwellide in his hows;
Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
30 and he hadde seuenti sones, that yeden out of his thiy, for he hadde many wyues.
Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
31 Forsothe a concubyn, `that is, secoundarie wijf, of hym, whom he hadde in Sichem, gendride to hym a sone, Abymelech bi name.
Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
32 And Gedeon, sone of Joas, diede in good elde, and was biried in the sepulcre of Joas, his fadir, in Ephra, of the meynee of Ezri.
Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
33 Forsothe aftir that Gedeon was deed, the sones of Israel turneden awey `fro Goddis religioun, and diden fornycacioun, `that is, idolatrie, with Baalym; and thei smytiden boond of pees with Baal, that he schulde be to hem in to God,
Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
34 nether thei hadden mynde of her Lord God, that delyuerede hem fro the hond of alle her enemyes `bi cumpas;
tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
35 nether thei diden merci with the hous of Gerobaal Gedeon, bi alle the goodis whiche he `hadde do to Israel.
Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.

< Judges 8 >