< Judges 4 >

1 And the sones of Israel addiden to do yuel in the `siyt of the Lord, aftir the deeth of Aioth.
Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
2 And the Lord bitook hem in to the hondis of Jabyn, kyng of Canaan, that regnede in Asor; and he hadde a duyk of his oost, Sisara bi name; and he dwellide in Aroseth of hethene men.
Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
3 And the sones of Israel crieden to the Lord; for he hadde nyn hundrid yrone charis, keruynge as sithis, and twenti yeer he oppresside hem greetli.
Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
4 Forsothe Delbora was a prophetesse, the wijf of Lapidoth, which Delbora demyde the puple in that tyme;
A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
5 and sche sat vndur a palm tree, that was clepid bi her name, bitwixe Rama and Bethel, in the hil of Effraym; and the sones of Israel stieden to hir at ech dom.
Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
6 And sche sente, and clepide Barach, the sone of Abynoen, of Cedes of Neptalym, and sche seide to hym, The Lord God of Israel comaundide to thee, Go thou, and lede an oost in to the hil of Thabor, and thou schalt take with thee ten thousande `of fiyteris of the sones of Neptalym and of the sones of Zabulon.
Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
7 Sotheli Y schal brynge to thee, in the place of the stronde of Cison, Sisara, prince of `the oost of Jabyn, and his charis, and al the multitude; and Y schal bitake hem in thin hond.
Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
8 And Barach seide to hir, If thou comest with me, Y schal go; if thou nylt come with me, Y schal not go.
Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
9 And sche seyde to hym, Sotheli Y schal go with thee; but in this tyme the victorie schal not be arettide to thee; for Sisara schal be bitakun in the hond of a womman. Therfor Delbora roos, and yede with Barach in to Cedes.
Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
10 And whanne Zabulon and Neptalym weren clepid, he stiede with ten thousynde of fiyteris, and hadde Delbora in his felouschipe.
a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
11 Forsothe Aber of Cyneth hadde departid sum tyme fro othere Cyneys hise britheren, sones of Obab, `alie of Moises; and he hadde set forth tabernaclis `til to the valei, which is clepid Sennym, and was bisidis Cedes.
To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
12 And it was teld to Sisara, that Barach, sone of Abynoen, hadde stiede in to the hil of Thabor.
Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
13 And he gaderide nyn hundrid yronne charis, keruynge as sithis, and al the oost fro Aroseth of hethene men to the stronde of Cison.
sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
14 And Delbora seide to Barach, Rise thou, for this is the day, in which the Lord bitook Sisara in to thin hondis; lo! the Lord is thi ledere. And so Barach cam doun fro the hil of Thabor, and ten thousynde of fyyteris with hym.
Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
15 And the Lord made aferd Sisara, and alle `the charis of hym, and al the multitude, bi the scharpnesse of swerd, at the siyt of Barach, in so myche that Sisara lippide doun of the chare, and fledde `a foote.
Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
16 And Barach pursuede the charis fleynge and the oost `til to Aroseth of hethene men; and al the multitude of enemyes felde doun `til to deeth.
Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
17 Sotheli Sisara fledde, and cam to the tente of Jahel, the wijf of Aber Cyney; forsothe pees waas bitwixe Jabyn, kyng of Asor, and bitwixe the hows of Aber Cyney.
Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
18 Therfor Jahel yede out in to the comyng of Sisara, and seide to hym, My lord, entre thou to me, entre thou to me; drede thou not. And he entride in to `the tabernacle of hir, and was hilid of hir with a mentil.
Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
19 And he seide to hir, Y biseche, yyue `thou to me a litil of watir, for Y thirste greetli. And sche openyde a `botel of mylk, and yaf to hym to drynke, and hilide hym.
Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
20 And Sisara seide to hir, Stonde thou bifor the dore of the tabernacle, and whanne ony man cometh, and axith thee, and seith, Whether ony man is here? thou schalt answere, No man is here.
Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
21 And so Jahel, the wijf of Aber, took a nayl of the tabernacle, and sche took also an hamer; and sche entride pryueli, and puttide with silence the nail on the temple of his heed, and sche fastnede the nail smytun with the hamer in to the brayn, `til to the erthe; and he slepte, and diede to gidere, and failide, and was deed.
Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
22 And lo! Barach suede Sisara, `and cam; and Jahel yede out in to his comyng, and seide to hym, Come, and Y schal schewe to thee the man, whom thou sekist. And whanne he hadde entrid to hir, he siy Sisara liggynge deed, and a nail fastnede in to hise templis.
Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
23 Therfor in that day God `made low Jabyn, the kyng of Canaan, bifor the sones of Israel;
A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
24 whiche encresiden ech dai, and with strong hond oppressiden Jabyn, the kyng of Canaan, til thei diden hym awey.
Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.

< Judges 4 >