< Judges 3 >

1 These ben the folkis whiche the Lord lefte, that in hem he schulde teche Israel, and alle men that knewen not the batels of Cananeis;
Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
2 and that aftirward `the sones of hem schulden lerne to fiyte with enemyes,
(ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
3 and to haue custom of batel He lefte fyue princes of Filistees, and al Cananei, and the puple of Sidon, and Euey that dwelliden in the hil Liban, fro the hil Baal Hermon `til to the entryng of Emath.
sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
4 And he lefte hem, that in hem he schulde asaie Israel, whethir thei wolden here the `heestis of the Lord, whiche he comaundide to her fadris bi the hond of Moises, ethir nai.
An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
5 And so the sones of Israel dwelliden in the myddis of Cananei, of Ethei, and of Ammorrei, and of Feresei, and of Euey,
Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
6 and of Jebusey, and weddiden wyues, the douytris of hem; and the sones of Israel yauen her douytris to `the sones of hem, and serueden `the goddis of hem.
Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
7 And the sones of Israel diden yuel in the `siyt of the Lord, and foryaten her Lord God, and serueden Baalym, and Astaroth.
Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
8 And the Lord was wrooth ayens Israel, and bitook hem in to the hondis of Cusanrasathaym, kyng of Mesopotanye, and thei serueden hym eiyte yeer.
Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
9 And thei crieden to the Lord, and he reiside to hem a sauyour, and delyuerede hem, that is, Othonyel, sone of Ceneth, `the lesse brothir of Caleph.
Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
10 And the spirit of the Lord was in hym, and he demyde Israel. And he yede out to batel, and the Lord bitook in to hise hondis Cusanrathaym, kyng of Sirie; and Othonyel oppresside hym.
Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
11 And the lond restide fourti yeer; and Othonyel, sone of Ceneth, diede.
Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
12 Forsothe the sones of Israel addiden to do yuel in the `siyt of the Lord; and he coumfortide ayens hem Eglon, the kyng of Moab, for `thei diden yuel in the `siyt of the Lord.
Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
13 And the Lord couplide to hym the sones of Amon and Amalech; and he yede, and smoot Israel, and hadde in possessioun the citee of Palmes.
Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
14 And the sones of Israel serueden Eglon, kyng of Moab, eiytene yeer.
Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
15 And aftirward thei crieden to the Lord; and he reiside to hem a sauyour, Aioth bi name, the sone of Gera, sone of Gemyny, which Aioth vside euer either hond for the riyt hond. And the sones of Israel senten bi him yiftis, `that is, tribute, to Eglon, kyng of Moab;
Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
16 which Aioth made to hym a swerd keruynge on euer either side, hauynge in the myddis a pomel of the lengthe of the pawm of an hond; and he was gird therwith vndir `the sai, `that is, a knyytis mentil, `in the riyt hipe.
To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
17 And he brouyte yiftis to Eglon, the kyng of Moab; forsothe Eglon was ful fat.
Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
18 And whanne he hadde youe yiftis to the kyng, he pursuede felowis that camen with hym; and he turnede ayen fro Galgalis,
Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
19 where idolis weren, and he seide to the kyng, A kyng, Y haue a priuei word to thee. And he comaundide silence. And whanne alle men weren goon out, that weren aboute hym, Aioth entride to hym;
A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
20 forsothe he sat aloone in a somer parlour. And Aioth seide, Y haue the word of God to thee.
Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
21 Which roos anoon fro the trone. And Aioth helde forth the left hond, and took the swerd fro his riyt hype; and he
Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
22 fastnede in to the `wombe of the kyng so strongli, that the pomel, `ether hilte, suede the yrun in the wounde, and was holdun streite `in the thickeste fatnesse with ynne; and he drow not out the swerd, but so as he hadde smyte, he lefte in the bodi; and anoon bi the priuetees of kynde the tordis of the wombe braste out.
Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
23 Forsothe whanne the doris of the parlour weren closid moost diligentli, and fastned with lok,
Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
24 Aioth yede out bi a posterne. And the `seruauntis of the king entriden, not in the parlour, but in the porche, and thei sien the doris of the parlour closid, and seiden, In hap he purgith the wombe in the somer parlour.
Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
25 And thei abididen longe, til thei weren aschamed; and thei sien that no man openede, and thei token the keie, and thei openyden, and founden her lord liggynge deed in the erthe.
Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
26 Sotheli while thei weren disturblid, Aioth fledde out, and passide the place of idols, fro whennus he turnede ayen; and he cam in to Seirath.
Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
27 And anoon he sownede with a clarioun in the hil of Effraym; and the sones of Israel camen doun with hym, and he yede in the frount.
Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
28 Which seide to hem, Sue ye me, for the Lord hath bitake oure enemyes, Moabitis, in to oure hondis. And thei camen doun after hym, and ocupieden the forthis of Jordan, that ledde ouer in to Moab.
Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
29 And thei suffriden not ony man to passe, but thei smytiden Moabitis in that tyme aboute ten thousande, alle myyti men and stronge; no man of hem myyte ascape.
A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
30 And Moab was maad low in that dai vndur the hond of Israel, and the lond restide fourescoor yeer.
A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
31 Aftir hym was Samgar, the sone of Anath, that smoot of Filisteis sixe hundrid men with a schar; and he also defendide Israel.
Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.

< Judges 3 >