< Judges 21 >

1 Also the sones of Israel sworen in Maspha, and seiden, Noon of vs schal yyue to the sones of Beniamyn a wijf of his douytris.
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 And `alle camen to the hows of God in Silo, and thei saten in the `siyt of hym `til to euentid, and thei reisiden the vois, and bigunnen to wepe with greet yellyng,
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 and seiden, Lord God of Israel, whi is this yuel don in thi puple, that to dai o lynage be takun awey of vs?
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 Sotheli in the tother day thei risiden eerli, and bildyden an auter, and offriden there brent sacrifices and pesible sacrifices, and seiden,
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 Who of alle the lynagis of Israel stiede not in to the oost of the Lord? For whanne thei weren in Maspha, thei `hadden bounde hem silf with a greuouse ooth, that thei that failiden schulden be slayn.
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 And the sones of Israel weren led bi penaunce on her brother Beniamyn, and bigunnen to seie, O lynage of Israel is takun awey;
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 wherof schulen thei take wyues? for alle we sworen in comyn, that we schulen not yyue oure douytris to hem.
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 Therfor thei seiden, Who is of alle the lynagis of Israel, that stiede not to the Lord in Maspha? And lo! the dwelleris of Jabes of Galaad weren foundun, that thei weren not in the oost.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 Also in that tyme, whanne thei weren in Silo, noon of hem was foundun there.
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 Therfor thei senten ten thousynde strongeste men, and comaundiden to hem, Go ye, and smyte the dwelleris of Jabes of Galaad bi the scharpnesse of swerd, as wel the wyues as `the litle children of hem.
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 And this thing schal be, which ye `owen to kepe, sle ye alle of male kynde, and the wymmen, that knewen men fleischli; reserue ye the virgyns.
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 And foure hundrid virgyns, that knewen not the bed of man, weren foundun of Jabes of Galaad; and thei brouyten hem to the castels in Silo, in to the lond of Chanaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 And `thei senten messangeris to the sones of Beniamyn, that weren in the stoon of Remmon; and thei comaundiden to hem, that thei schulden resseyue tho wymmen in pees.
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 And the sones of Beniamyn camen in that tyme, and the douytris of Jabes of Galaad weren youun to hem to wyues; forsothe thei founden not othere wymmen, whiche thei schulden yyue in lijk maner.
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 And al Israel sorewide greetly, and dide penaunce on the sleyng of o lynage of Israel.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 And the grettere men in birthe seiden, What schulen we do to the othere men, that han not take wyues? Alle the wymmen in Beniamyn felden doun,
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 and it `is to vs to puruey `with greet cure and greet studie, that o lynage be not don awey fro Israel.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 We moun not yyue oure douytris to hem, for we ben boundun with an ooth and cursyng, bi which we seiden, Be he cursid that yyueth of hise douytris a wijf to Beniamyn.
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 And thei token a counsel, and seiden, Lo! annyuersarie solempnyte of the Lord is in Silo, whych is set at the north of the citee of Bethel, and at the eest coost of the weie that goith from Bethel to Siccyma, and at the south of the citee of Lebona.
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 And thei comaundiden to the sones of Beniamyn, and seiden, Go ye, be ye hid in the vyneris;
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 and whanne ye seen douytris of Silo go forth bi custom to lede daunsis, go ye out of the vyneris sudeynli, and rauysche ye hem, eche man o wijf, and go ye in to the lond of Beniamyn.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 And whanne the fadris and britheren of hem schulen come, and bigynne to pleyne and plete ayens you, we schulen seie to hem, Haue ye mercy of hem; for thei rauyschiden not hem bi riyt of fiyteris and ouercomeris, but ye `yauen not to hem preiynge that thei schulden take; and the synne is of youre part.
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 And the sones of Beniamyn diden as it was comaundid to hem, and bi her noumbre thei rauyschiden wyues to hem, ech man o wijf, of hem that ledden daunsis. And thei yeden in to her possessioun, and bildiden citees, and dwelliden in tho.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 And the sones of Israel turneden ayen, bi lynagis and meynees, in to her tabernaclis.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 In tho dayes was no kyng in Israel, but ech man dide this, that semyde ryytful to hym silf.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.

< Judges 21 >