< Judges 15 >

1 `Forsothe aftir sum del of tyme, whanne the daies of wheete heruest neiyiden, Sampson cam, and wolde visite his wijf, and he brouyte to hir a `kide of geet; and when he wolde entre in to hir bed bi custom, `the fadir of hir forbeed hym, and seide,
Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
2 Y gesside that thou haddist hatid hir, and therfor Y yaf hir to thi freend; but sche hath a sistir, which is yongere and fairere than sche, be sche `wijf to thee for hir.
Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
3 To whom Sampson answeride, Fro this day no blame schal be in me ayens Filistees, for Y schal do yuels to you.
Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
4 And he yede, and took thre hundrid foxis, and ioynede `the tailis of hem to tailis, and boond brondis in the myddis,
Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
5 whiche he kyndlid with fier, and leet hem, that thei schulden renne aboute hidur and thidur; `which yeden anoon in to the cornes of Filisteis, bi whiche kyndlid, bothe cornes `borun now to gidere, and yit stondynge in the stobil, weren brent, in so myche that the flawme wastide vyneris, and `places of olyue trees.
sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
6 And Filisteis seiden, Who dide this thing? To whiche it was seid, Sampson, hosebonde of the `douytir of Thannathei, for he took awey Sampsones wijf, and yaf to another man, `wrouyte this thing. And Filisteis stieden, and brenten bothe the womman and hir fadir.
Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
7 To whiche Sampson seide, Thouy ye han do this, netheles yit Y schal axe veniaunce of you, and than Y schal reste.
Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
8 And he smoot hem with greet wounde, so that thei wondriden, and `puttiden the hyndrere part of the hipe on the thiy; and he yede doun, and dwellide in the denne of the stoon of Ethan.
Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
9 Therfor Filisteis stieden in to the lond of Juda, and settiden tentis in the place, that was clepid aftirward Lethi, that is, a cheke, wher `the oost of hem was spred a brood.
Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
10 And men of the lynage of Juda seiden to hem, Whi `stieden ye ayens vs? Whiche answeriden, We comen that we bynde Sampson, and yelde to hym tho thingis whiche he wrouyte in vs.
Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
11 Therfor thre thousynde of men of Juda yeden doun to the denne of the flynt of Ethan; and thei seiden to Sampson, Woost thou not, that Filisteis comaunden to vs? Why woldist thou do this thing? To whiche he seide.
Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
12 As thei diden to me, Y dide to hem. Thei seien, We comen to bynde thee, and to bitake thee in to the `hondis of Filisteis. To whiche Sampson answeride, Swere ye, and `biheete ye to me, that ye sle not me.
Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
13 And thei seiden, We schulen not sle thee, but we schulen bitake thee boundun. And thei bounden him with twei newe cordis, and token fro the stoon of Ethan.
Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
14 And whanne thei hadden come to the place of cheke, and Filisteis criynge hadden runne to hym, the spirit of the Lord felde in to hym, and as stikis ben wont to be wastid at the odour of fier, so and the bondis, with whiche he was boundun, weren scaterid and vnboundun.
Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
15 And he took a cheke foundun, that is, the lowere cheke boon of an asse, that lay, `and he killyde `with it a thousinde men; and seide,
Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
16 With the cheke of an asse, that is, with the lowere cheke of a colt of femal assis, Y dide hem awey, and Y killide a thousynde men.
Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
17 And whanne he songe these wordis, and `hadde fillid, he castide forth fro the hond the lowere cheke; and he clepide the name of that place Ramath Lethi, `which is interpretid, the reisyng of a cheke.
Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
18 And he thristide greetly, and criede to the Lord, and seide, Thou hast youe in the hond of thi seruaunt this grettest helthe and victory; and lo! Y die for thyrst, and Y schal falle in to the hondis of vncircumcidid men.
Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
19 Therfor the Lord openyde a wang tooth in the cheke boon of the asse, and watris yeden out therof, `bi whiche drunkun he refreischide the spirit, and resseuede strengthis; therfor the name of that place was clepid the Welle of the clepere of the cheke `til to present dai.
Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
20 And he demyde Israel in the daies of Filistiym twenti yeer.
Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.

< Judges 15 >