< Joshua 2 >
1 Therfor Josue, the sone of Nun, sente fro Sethym twei men, aspieris in hiddlis, and seide to hem, Go ye, and biholde ye the lond, and the citee of Jerico. Whiche yeden, and entriden into the hous of a womman hoore, `Raab bi name, and restiden at hir.
Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
2 And it was teld, `and seid to the kyng of Jerico, Lo! men of the sones of Israel entriden hidir bi nyyt, to aspie the lond.
Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
3 Therfor the kyng of Jerico sente to Raab the hoore, and seide, Brynge out the men, that camen to thee, and entriden in to thin hous; for thei ben aspieris, and thei camen to biholde al the lond.
Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
4 And the womman took the men, and hidde hem, and seide, Y knowleche, thei camen to me, but Y wiste not of whenus thei weren;
Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
5 and whanne the yate was closid in derknessis, and thei yeden out to gidire, Y noot whidur thei yeden; pursue ye soone, and ye schulen take hem.
da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
6 Forsothe sche made the men to stie in to the soler of hir hows, and hilide hem with stobil of flex, that was there.
(Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
7 Sotheli thei, that weren sent, sueden hem bi the weie that ledith to the fordis of Jordan; and whanne thei weren goon out, anoon the yate was closid.
Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
8 Thei that weren hid, slepten not yit, and lo! the womman stiede to hem, and seide,
Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
9 Y knowe that the Lord hath bitake to you this lond; for youre feerdfulnesse felde in to vs, and alle the dwelleris of the lond `weren sike.
ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
10 We herden, that the Lord driede the watris of the Reed See at youre entryng, whanne ye yeden out of Egipt; and what thingis ye diden to twei kyngis of Ammorreis, that weren biyende Jordan, to Seon and Og, whiche ye killiden;
Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
11 and we herden these thingis, and we dredden, and oure herte `was sike, and spirit dwellide not in vs at youre entryng; for youre Lord God hym silf is God in heuene aboue, and in erthe bynethe.
Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
12 Now therfor swere ye to me bi the Lord God, that as Y dide merci with you, so and ye do with the hows of my fadir; and yyue ye to me a veri signe,
Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
13 that ye saue my fadir and modir, and my britheren and sistris, and alle thingis that ben herne, and dilyuere oure lyues fro deeth.
za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
14 Whiche answeriden to hir, Oure lijf be for you in to deeth, if netheles thou bitraiest not vs; and whanne the Lord hath bitake to vs the lond, we schulen do mercy and treuthe in thee.
Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
15 Therfor sche let hem doun fro the wyndow bi a corde; for hir hows cleuyde to the wal.
Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
16 And sche seide to hem, Stie ye to the hilli places, lest perauenture men turnynge ayen meete you; and be ye hidde there three daies, til thei comen ayen; and so ye schulen go bi youre weie.
Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
17 Whiche seiden to hir, We schulen be giltles of this ooth, bi which thou hast chargid vs,
Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
18 if, whanne we entren in to the lond, this reed corde is not a signe, and thou byndist it not in the wyndow, bi which thou lettist vs doun; and thou gaderist not in to thi hows thi fadir and modir, and britheren, and al thi kynrede; the blood of hym schal be on his heed,
sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
19 that goith out at the dore of thin hows, and we schulen be alien, that is, giltles; forsothe the blood of alle men that ben in the hows with thee, schal turne in to oure heed, if ony man touchith hem.
In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
20 `That if thou wolt betraie vs, and brynge forth in to the myddis this word, we schulen be cleene of this ooth, bi which thou hast chargid vs.
In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
21 And sche answeride, As ye han spoke, so be it doon. And sche lefte hem, that thei schulden go, and sche hangide a reed corde in her wyndow.
Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
22 Sotheli thei yeden, and camen to the hilli places, and dwelliden there three daies, til thei turneden ayen that pursueden; for thei souyten bi ech weie, and founden not hem.
Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
23 And whanne the sekeris entriden in to the citee, the spieris turneden ayen, and camen doun fro the hille; and whanne thei hadde passid Jordan, thei camen to Josue, the sone of Nun;
Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
24 and thei telden to hym alle thingis that bifelden to hem, and seiden, The Lord hath bitake al the lond in to oure hondis, and alle the dwelleris thereof ben casten doun bi drede.
Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”