< Joshua 19 >

1 And the secounde lot of the sones of Symeon yede out, bi her meynees; and the eritage of hem,
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 in the myddis of possessioun of the sones of Juda, was Bersabee, and Sabee,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 and Melada, and Asersua, Bala,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 and Asem, and Betholaad, Bethularma, and Siceleth,
Eltolad, Betul, Horma,
5 and Bethmarchaboth, and Asersua,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 and Bethelebaoth, and Saroem, threttene citees, and `the townes of tho;
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 Aym, and Remmon, and Athar, and Asam, foure citees, and `the townes of tho; alle the townes bi cumpas of these citees,
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 `til to Balath Brameth, ayens the south coost, weren seuentene citees. This is the eritage of the sones of Symeon, bi her meynees,
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 in the possessioun and part of the sones of Juda, for it was more; and therfor the sones of Symeon hadden possessioun in the myddis of the eritage therof.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 And the thridde lot of the sones of Zabulon felde, bi her meynees; and the terme of possessioun of the sones of Zabulon was maad `til to Sarith;
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 and it stieth fro the see, and Medala; and it cometh in to Debbaseth, `til to the stronde which is ayens Jecenam;
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 and it turneth ayen fro Sarith, ayens the eest, in to the coostis of Sechelech Tabor; and goith out to Daberth; and it stieth ayens Jasie;
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 and fro thennus it passith to the eest coost to Gethefer, and Thacasym; and it goith out in to Remmon, Amphar, and Noa; and cumpassith to the north, and Nachon;
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 and the goyngis out therof ben the valei of Jeptael,
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 and Cathel, and Neamai, and Semrom, and Jedaba, and Bethleem, twelue citees, and `the townes of tho.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 This is the eritage of the lynage of the sones of Zabulon, bi her meynees, and the citees and `townes of tho.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 The fourthe lot yede out to Isacar, bi hise meynees; and the eritage therof was Jezrael,
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 and Casseloth,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 and Symen, and Affraym, and Seon,
Hafarayim, Anaharat,
20 and Anaarath, and Cabith, and Cesion, Hames,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 and Ramech, and Enganym, and Enadda, and Bethfeses.
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 And the terme therof cometh `til to Tabor, and Seesyma, and Hethsemes; and the outgoyngis therof weren Jordan, sixtene citees, and `the townes of tho.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 This is the possessioun of the sones of Ysachar, bi her meynees, the citees and the townes of tho.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 And the fiuethe lot felde to the lynage of the sones of Aser, by her meynees;
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 and the terme of hem was Alchat, and Adi, and Bethen,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 and Mesaph, and Elmelech, and Amaad, and Messal; and it cometh `til to Carmel of the see, and Sior, and Labanath; and it turneth ayen,
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 ayens the eest, to Bethdagan; and passith `til to Zabulon, and to the valei of Jeptael, ayens the north, in Bethemeth, and Neyel; and it goith out to the left side to Gabul,
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 and Acran, and Roob, and Omynon, and Chane, `til to grete Sidon;
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 and it turneth ayen in to Horma, `til to the strongeste citee Tire, and `til to Ossam; and the outgoyngis therof schulen be in to the see, fro the part of Aczyma,
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 and Affeth, and Roob; two and twenti citees, and `the townes of tho.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 This is the possessioun of the sones of Aser, bi her meynees, `the citees, and `townes of tho.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 The sixte lot of the sones of Neptalym felde, bi her meynees;
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 and the terme bigan of Heleth, and Helon, and Sannaira, and Adarny, `which is Neceb, and Jebnael, `til to Letum; and the outgoyng of hem til to Jordan;
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 and the terme turneth ayen, ayens the west, in to Arnoth of Thabor; and fro thennus it goith out in to Hucota, and passith in to Zabulon, ayens the south, and in to Asor, ayens the west, and in to Juda, at Jordan, ayens the risyng of the sunne;
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 of the strongeste citee Assydym, Ser, and Amraath,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 and Rechath, Cenereth, and Edema,
Adama, Rama, Hazor,
37 and Arama, Asor, and Cedes, and Edrai,
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 Nason, and Jeron, and Magdael, Horem, and Bethanath, and Bethsemes; nyntene citees, and `the townes of tho.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 This is the possessioun of the lynage of the sones of Neptalym, bi her meynees, the citees, and the townes of tho.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 The seuenthe lot yede out to the lynage of the sones of Dan, bi her meynees;
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 and the terme of the possessioun therof was Saraa, and Ascahol, and Darsemes, that is, the citee of the sunne,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 Selenym, and Hailon, and Jethala,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 Helom, and Thenna, and Acrom,
Elon, Timna, Ekron,
44 Helthecem, Jebtom, and Baalath, Lud,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 and Benebarach, and `Jethremmon, and Ihercon,
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 and Arecon, with the terme that biholdith Joppen,
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 and is closid with that ende. And the sones of Dan stieden, and fouyten ayens Lesem; and thei token it, and smytiden it bi the scharpnes of swerd, and hadden in possessioun, and dwelliden therynne; and thei clepiden the name therof Lesan Dan, by the name of Dan, her fadir.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 This is the possessioun of the lynage of Dan, bi her meynees, the citees, and townes of tho.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 And whanne thei hadden fillid to departe the lond bi lot to alle men bi her lynagis, the sones of Israel yauen possessioun to Josue, sone of Nun,
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 in the myddis of hem, bi the comaundement of the Lord, the citee which he axide, Thannath Sara, in the hil of Effraym; and he bildide the citee, and dwellide therynne.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 These ben the possessiouns whiche Eleazar, preest, and Josue, sone of Nun, and the princis of meynees, and of the lynagis of the sones of Israel, departiden bi lot in Silo, bifor the Lord, at the dore of tabernacle of witnessing, and departiden the lond.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.

< Joshua 19 >