< Joshua 11 >

1 And whanne Jabyn, kyng of Asor, hadde herd these thingis, he sente to Jobab, kyng of Madian, and to the kyng of Semeron, and to the kyng of Acsaph; forsothe to the kyngis of the north,
Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
2 that dwelliden in the hilli places, and in the pleyn ayens the south of Seneroth, and in the feeldi places, and cuntreis of Dor, bisidis the see,
ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
3 and `to Cananei fro the eest and west, and to Ammorrey, and Ethei, and Feresei, and Jebusei, in the `hilli places, and to Euey, that dwellide at the rootis of Hermon, in the lond of Maspha.
ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
4 And alle yeden out with her cumpanyes, a ful myche puple, as the grauel which is in the `brynk of the see, and horsis, and charis, of greet multitude.
Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
5 And alle these kyngis camen togidere at the watris of Meron, to fiyte ayens Israel.
Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
6 And the Lord seyde to Josue, Drede thou not hem, for to morewe, in this same our, Y schal bitake alle these men to be woundid in the siyt of Israel; thou schalt hoxe `the horsis of hem, and thou schalt brenne `the charis bi fier.
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
7 And Josue cam, and al his oost with hym, ayens hem sodenli, at the watris of Meron, `and felden on hem.
Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
8 And the Lord bitook hem in to the hondis of Israel; whiche smytiden hem, `that is, the hethen kyngis and her oostes, and pursueden `til to grete Sidon, and the watris of Maserophoth, and to the feeld of Maspha, which is at the eest part therof. Josue smoot so alle men, that he lefte no relikis of hem;
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
9 and he dide as the Lord comaundide to hym; he hoxide `the horsis of hem, and brente the charis.
Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
10 And he turnede ayen anoon, and took Asor, and `smoot bi swerd the kyng therof; for Asor helde bi eld tyme the prinsehed among alle these rewmes.
A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
11 And `he smoot alle persoones that dwelliden there, he lefte not ony relikys therynne, but he wastide alle thingis `til to deeth; also he distriede thilke citee bi brennyng.
Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
12 And he took alle `citees bi cumpas, and `the kyngis of hem, and smoot, and dide awei, as Moises, the `seruaunt of the Lord,
Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
13 comaundide to hym, without citees that weren set in the grete hillis, and in litle hillis; and Israel brente the othere citees; flawme wastide oneli o citee, Asor, the strongeste.
Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
14 And the sones of Israel departiden to hem silf al the prei, and werk beestis of these citees, whanne alle men weren slayn.
Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
15 As the Lord comaundide to his seruaunt Moises, so Moises comaundide to Josue, and `he fillide alle thingis; he passide not of alle comaundementis, `nether o word sotheli, which the Lord comaundide to Moises.
Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
16 And so Josue took al the `lond of the hillis, and of the south, the lond of Gosen, and the pleyn, and the west coost, and the hil of Israel, and the feeldi places therof;
Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
17 and the part of the hil that stieth to Seir `til to Baalgath, bi the pleyn of Liban vndur the hil of Hermon; Josue took, and smoot, and killide alle the kyngis of tho places.
Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
18 Josue fauyt myche tyme ayens these kyngis;
Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
19 `no citee was, which bitook not it silf to the sones of Israel, out takun Euey that dwellide in Gabaon; he took alle bi batel.
Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
20 For it was the sentence of the Lord, that `the hertis of hem schulde be maad hard, and that thei schulden fiyte ayens Israel, and schulden falle, and schulden not disserue ony mercy, and schulden perische, as the Lord comaundide to Moises.
Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 Josue cam in that tyme, and killide Enachym, that is, giauntis, fro the `hilli placis of Ebron, and of Dabir, and of Anab, and fro al the hil of Juda, and of Israel, and dide awei `the citees of hem.
A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
22 He lefte not ony man of the generacioun of Enachim in the lond of the sones of Israel, without the citees of Gasa, and Geth, and Azotus, in whiche aloone thei weren left.
Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
23 Therfor Josue took al the lond, as the Lord spak to Moyses, and he yaf it in to possessioun to the sones of Israel, bi her partis and lynagis; and the lond restide fro batels.
Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.

< Joshua 11 >