< John 21 >

1 Afterward Jhesus eftsoone schewide hym to hise disciplis, at the see of Tiberias.
Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa:
2 And he schewide him thus. There weren togidere Symount Petre, and Thomas, that is seid Didimus, and Nathanael, that was of the Cane of Galilee, and the sones of Zebedee, and tweyne othere of hise disciplis.
Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu.
3 Symount Petre seith to hem, Y go to fische. Thei seyn to hym, And we comen with thee. And `thei wenten out, `and wenten in to a boot. And in that niyt thei token no thing.
Saminu Bitrus yace masu, “Zani su.” sukace masa “Mu ma za mu je tare da kai.” Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.
4 But whanne the morewe was comun, Jhesus stood in the brenke; netheles the disciplis knewen not, that it was Jhesus.
To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane.
5 Therfor Jhesus seith to hem, Children, whethir ye han ony souping thing? Thei answeriden to hym, Nay. He seide to hem,
Sai Yesu yace masu, “Samari, kuna da wani abinda za a ci?” Suka amsa masa sukace “A'a”.
6 Putte ye the nett in to the riyt half of the rowing, and ye schulen fynde. And thei puttiden the nett; and thanne thei miyten not drawe it for multitude of fischis.
Yace masu, “Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu.” Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.
7 Therfor thilke disciple, whom Jhesus louede, seide to Petre, It is the Lord. Symount Petre, whanne he hadde herd that it is the Lord, girte hym with a coote, for he was nakid, and wente in to the see.
Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, “Ubangiji ne fa!” Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun.
8 But the othere disciplis camen bi boot, for thei weren not fer fro the lond, but as a two hundrid cubitis, drawinge the nett of fischis.
Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi.
9 And as thei camen doun in to the lond, thei sayn coolis liynge, and a fisch leid on, and breed.
Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.
10 Jhesus seith to hem, Bringe ye of the fyschis, whiche ye han takun now.
Yesu ya ce masu “Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu”.
11 Symount Petre wente vp, and drowy the nett in to the lond, ful of grete fischis, an hundrid fifti and thre; and whanne thei weren so manye, the nett was not brokun.
Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.
12 Jhesus seith to hem, Come ye, ete ye. And no man of hem that saten at the mete, durste axe hym, Who art thou, witinge that it is the Lord.
Yesu yace masu, “Ku zo ku karya kumallo”. Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa “Ko shi wanene?” Domin sunsani Ubangiji ne.
13 And Jhesus cam, and took breed, an yaf to hem, and fisch also.
Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin.
14 Now this thridde tyme Jhesus was schewid to hise disciplis, whanne he hadde risun ayen fro deth.
Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.
15 And whanne thei hadde etun, Jhesus seith to Simount Petre, Symount of Joon, louest thou me more than these? He seith to him, Yhe, Lord, thou woost that Y loue thee. Jhesus seith to hym, Fede thou my lambren.
Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, “Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?” Bitrus yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka” Yesu yace masa “Ka ciyar da 'ya'yan tumakina”.
16 Eft he seith to hym, Symount of Joon, louest thou me? He seith to him, Yhe, Lord, thou woost that Y loue thee. He seith to him, Fede thou my lambren.
Ya sake fada masa karo na biyu, “Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?” Bitrus Yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka”. Yesu yace masa, “Ka lura da Tumakina”.
17 He seith to him the thridde tyme, Simount of Joon, louest thou me? Petre was heuy, for he seith to hym the thridde tyme, Louest thou me, and he seith to him, Lord, thou knowist alle thingis; thou woost that Y loue thee. Jhesus seith to hym, Fede my scheep.
Ya sake fada masa, karo na uku, “Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, “Kana kaunata” Yace masa, “Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka.” Yesu yace masa “Ka ciyar da tumaki na.
18 Treuli, treuli, Y seie to thee, whanne thou were yongere, thou girdidist thee, and wandridist where thou woldist; but whanne thou schalt waxe eldere, thou schalt holde forth thin hondis, and another schal girde thee, and schal lede thee whidur thou wolt not.
Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba.”
19 He seide this thing, signifynge bi what deth he schulde glorifie God. And whanne he hadde seid these thingis, he seith to hym, Sue thou me.
To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.
20 Petre turnede, and say thilke disciple suynge, whom Jhesus louede, which also restid in the soper on his brest, and he seide to hym, Lord, who is it, that schal bitraie thee?
Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace “Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?”
21 Therfor whanne Petre hadde seyn this, he seith to Jhesu, Lord, but what this?
Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu “Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?”
22 Jhesus seith to him, So I wole that he dwelle til that Y come, what to thee? sue thou me.
Yesu yace masa, “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni.”
23 Therfor this word wente out among the britheren, that thilke disciple dieth not. And Jhesus seide not to hym, that he dieth not, but, So Y wole that he dwelle til Y come, what to thee?
Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?”
24 This is thilke disciple, that berith witnessyng of these thingis, and wroot hem; and we witen, that his witnessyng is trewe.
Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne.
25 And ther ben also manye othere thingis that Jhesus dide, whiche if thei ben writun bi ech bi hym silf, Y deme that the world hym silf schal not take tho bookis, that ben to be writun.
Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.

< John 21 >