< Joel 3 >
1 For lo! in tho daies, and in that tyme, whanne Y schal turne the caitifte of Juda and of Jerusalem,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 Y schal gadere alle folkis, and Y schal lede hem in to the valei of Josephat; and Y schal dispute there with hem on my puple, and myn eritage Israel, whiche thei scateriden among naciouns; and thei departiden my lond, and senten lot on my puple;
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 and thei settiden a knaue child in the bordel hous, and seelden a damesel for wyn, that thei schulden drynke.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 But what to me and to you, thou Tire, and Sidon, and ech ende of Palestyns? Whethir ye schulen yelde vengyng to me? and if ye vengen you ayens me, soone swiftli Y schal yelde while to you on youre heed.
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 Ye token awey my siluer and gold, and ye brouyten my desirable thingis and faireste thingis in to youre templis of idols.
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 And ye selden the sones of Juda, and the sones of Jerusalem to the sones of Grekis, that ye schulden make hem fer fro her coostis.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Lo! Y schal reise hem fro the place in which ye seelden hem; and Y schal turne youre yeldyng in to youre heed.
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 And Y schal sille youre sones and youre douytris in the hondis of the sones of Juda, and thei schulen selle hem to Sabeis, a fer folc, for the Lord spak.
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 Crye ye this thing among hethene men, halewe ye batel, reise ye stronge men; alle men werriours, neiy, and stie.
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 Beete ye togydere youre plowis in to swerdis, and youre mattokkis in to speeris; a sijk man seie, that Y am strong.
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 Alle folkis, breke ye out, and come fro cumpas, and be ye gaderid togidere; there the Lord schal make thi stronge men to die.
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 Folkis rise togidere, and stie in to the valei of Josofat; for Y schal sitte there, to deme alle folkis in cumpas.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 Sende ye sikelis, `ether sithis, for ripe corn wexide; come ye, and go ye doun, for the pressour is ful; pressouris ben plenteuouse, for the malice of hem is multiplied.
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Puplis, puplis in the valei of kittyng doun; for the dai of the Lord is nyy in the valei of kittyng doun.
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 The sunne and the moone ben maad derk, and sterris withdrowen her schynyng.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 And the Lord schal rore fro Sion, and schal yyue his vois fro Jerusalem, and heuenes and erthe schulen be mouyd; and the Lord is the hope of his puple, and the strengthe of the sones of Israel.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 And ye schulen wite, that Y am youre Lord God, dwellynge in Sion, in myn hooli hil; and Jerusalem schal be hooli, and aliens schulen no more passe bi it.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 And it schal be, in that dai mounteyns schulen droppe swetnesse, and litle hillis schulen flowe with mylke, and watris schulen go bi alle the ryueris of Juda; and a welle schal go out of the hous of the Lord, and schal moiste the stronde of thornes.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 Egipt schal be in to desolacioun, and Idume in to desert of perdicioun; for that that thei diden wickidli ayens the sones of Juda, and schedden out innocent blood in her lond.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 And Judee schal be enhabited with outen ende, and Jerusalem in to generacioun and in to generacioun.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 And Y schal clense the blood of hem, which Y hadde not clensid; and the Lord schal dwelle in Syon.
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”