< Job 6 >
1 Forsothe Joob answeride, and seide,
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Y wolde, that my synnes, bi whiche Y `desseruede ire, and the wretchidnesse which Y suffre, weren peisid in a balaunce.
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 As the grauel of the see, this wretchidnesse schulde appere greuousere; wherfor and my wordis ben ful of sorewe.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 For the arowis of the Lord ben in me, the indignacioun of whiche drynkith vp my spirit; and the dredis of the Lord fiyten ayens me.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Whether a feeld asse schal rore, whanne he hath gras? Ethir whether an oxe schal lowe, whanne he stondith byfor a `ful cratche?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Ether whethir a thing vnsauery may be etun, which is not maad sauery bi salt? Ether whether ony man may taaste a thing, which tastid bryngith deeth?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 For whi to an hungri soule, yhe, bittir thingis semen to be swete; tho thingis whiche my soule nolde touche bifore, ben now my meetis for angwisch.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Who yyueth, that myn axyng come; and that God yyue to me that, that Y abide?
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 And he that bigan, al to-breke me; releesse he his hond, and kitte me doun?
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 And `this be coumfort to me, that he turmente me with sorewe, and spare not, and that Y ayenseie not the wordis of the hooli.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 For whi, what is my strengthe, that Y suffre? ethir which is myn ende, that Y do pacientli?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Nethir my strengthe is the strengthe of stoonus, nether my fleisch is of bras.
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Lo! noon help is to me in me; also my meyneal frendis `yeden awey fro me.
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 He that takith awei merci fro his frend, forsakith the drede of the Lord.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 My britheren passiden me, as a stronde doith, that passith ruschyngli in grete valeis.
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Snow schal come on hem, that dreden frost.
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 In the tyme wherynne thei ben scaterid, thei schulen perische; and as thei ben hoote, thei schulen be vnknyt fro her place.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 The pathis of her steppis ben wlappid; thei schulen go in veyn, and schulen perische.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Biholde ye the pathis of Theman, and the weies of Saba; and abide ye a litil.
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 Thei ben schent, for Y hopide; and thei camen `til to me, and thei ben hilid with schame.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Now ye ben comun, and now ye seen my wounde, and dreden.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Whether Y seide, Brynge ye to me, and yiue ye of youre catel to me? ethir,
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Delyuere ye me fro the hond of enemy, and rauysche ye me fro the hond of stronge men?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Teche ye me, and Y schal be stille; and if in hap Y vnknew ony thing, teche ye me.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Whi han ye depraued the wordis of trewthe? sithen noon is of you, that may repreue me.
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Ye maken redi spechis oneli for to blame, and ye bryngen forth wordis in to wynde.
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 Ye fallen in on a fadirles child, and enforsen to peruerte youre frend.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Netheles fille ye that, that ye han bigunne; yyue ye the eere, and se ye, whether Y lie.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Y biseche, answere ye with out strijf, and speke ye, and deme ye that, that is iust.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 And ye schulen not fynde wickidnesse in my tunge, nethir foli schal sowne in my chekis.
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?