< Job 34 >

1 And Helyu pronounside, and spak also these thingis,
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Wise men, here ye my wordis, and lerned men, herkne ye me; for the eere preueth wordis,
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 and the throte demeth metis bi taast.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Chese we doom to vs; and se we among vs, what is the betere.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 For Job seide, Y am iust, and God hath distried my doom.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 For whi lesynge is in demynge me, and myn arowe is violent with out ony synne.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Who is a man, as Joob is, that drynkith scornyng as watir?
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 that goith with men worchynge wickidnesse, and goith with vnfeithful men?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For he seide, A man schal not plese God, yhe, thouy he renneth with God.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Therfor ye men hertid, `that is, vndurstonde, here ye me; vnpite, `ethir cruelte, be fer fro God, and wickidnesse fro Almyyti God.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 For he schal yelde the werk of man to hym; and bi the weies of ech man he schal restore to hym.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 For verili God schal not condempne with out cause; nether Almyyti God schal distrie doom.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 What othere man hath he ordeyned on the lond? ether whom hath he set on the world, which he made?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 If God dressith his herte to hym, he schal drawe to hym silf his spirit and blast.
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Ech fleisch schal faile togidere; `and a man schal turne ayen in to aisch.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Therfor if thou hast vndurstondyng, here thou that that is seid, and herkne the vois of my speche.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Whether he that loueth not doom may be maad hool? and hou condempnest thou so myche him, that is iust?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Which seith to the kyng, Thou art apostata; which clepith the duykis vnpitouse, `ethir vnfeithful.
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 `Which takith not the persoones of princes, nether knew a tyraunt, whanne he stryuede ayens a pore man; for alle men ben the werk of hise hondis.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 Thei schulen die sudeynli, and at mydnyyt puplis schulen be troblid, `ethir schulen be bowid, as othere bookis han; and schulen passe, and schulen take `awei `a violent man with out hond.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For the iyen of God ben on the weies of men, and biholdith alle goyngis of hem.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 No derknessis ben, and no schadewe of deeth is, that thei, that worchen wickidnesse, be hid there;
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 for it is `no more in the power of man, that he come to God in to doom.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 God schal al to-breke many men and vnnoumbrable; and schal make othere men to stonde for hem.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 For he knowith the werkis of hem; therfor he schal brynge yn niyt, and thei schulen be al to-brokun.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 He smoot hem, as vnpitouse men, in the place of seinge men.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Whiche yeden awei fro hym bi `castyng afore, and nolden vndurstonde alle hise weies.
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 That thei schulden make the cry of a nedi man to come to hym, and that he schulde here the vois of pore men.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 For whanne he grauntith pees, who is that condempneth? Sithen he hidith his cheer, who is that seeth hym? And on folkis and on alle men `he hath power `to do siche thingis.
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Which makith `a man ypocrite to regne, for the synnes of the puple.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Therfor for Y haue spoke to God, also Y schal not forbede thee.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 If Y erride, teche thou me; if Y spak wickidnesse, Y schal no more adde.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Whether God axith that wickidnesse of thee, for it displeside thee? For thou hast bigunne to speke, and not Y; that if thou knowist ony thing betere, speke thou.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Men vndurstondynge, speke to me; and a wise man, here me.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Forsothe Joob spak folili, and hise wordis sownen not techyng.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 My fadir, be Joob preuede `til to the ende; ceesse thou not fro the man of wickidnesse,
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 `that addith blasfemye ouer hise synnes. Be he constreyned among vs in the meene tyme; and thanne bi hise wordis stire he God to the doom.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >