< Job 31 >

1 I made couenaunt with myn iyen, that Y schulde not thenke of a virgyn.
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 For what part schulde God aboue haue in me, and eritage Almyyti God of hiye thingis?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Whether perdicioun is not to a wickid man, and alienacioun of God is to men worchynge wickidnesse?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Whether he biholdith not my weies, and noumbrith alle my goyngis?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 If Y yede in vanyte, and my foot hastide in gile,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 God weie me in a iust balaunce, and knowe my symplenesse.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 If my step bowide fro the weie; if myn iye suede myn herte, and a spotte cleuede to myn hondis;
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 sowe Y, and another ete, and my generacioun be drawun out bi the root.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 If myn herte was disseyued on a womman, and if Y settide aspies at the dore of my frend; my wijf be the hoore of anothir man,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 and othir men be bowid doun on hir.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 For this is vnleueful, and the moost wickidnesse.
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Fier is deourynge `til to wastyng, and drawynge vp bi the roote alle generaciouns.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 If Y dispiside to take doom with my seruaunt and myn hand mayde, whanne thei stryueden ayens me.
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 What sotheli schal Y do, whanne God schal rise to deme? and whanne he schal axe, what schal Y answere to hym?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Whether he, that wrouyte also hym, made not me in the wombe, and o God formede me in the wombe?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 If Y denyede to pore men that, that thei wolden, and if Y made the iyen of a wydewe to abide;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 if Y aloone eet my mussel, and a faderles child eet not therof;
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 for merciful doyng encreesside with me fro my yong childhed, and yede out of my modris wombe with me;
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 if Y dispiside a man passynge forth, for he hadde not a cloth, and a pore man with out hilyng;
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 if hise sidis blessiden not me, and was not maad hoot of the fleeces of my scheep;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 if Y reiside myn hond on a fadirles child, yhe, whanne Y siy me the hiyere in the yate;
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 my schuldre falle fro his ioynt, and myn arm with hise boonys be al to-brokun.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 For euere Y dredde God, as wawis wexynge gret on me; and `Y myyte not bere his birthun.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 If Y gesside gold my strengthe, and if Y seide to purid gold, Thou art my trist;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 if Y was glad on my many ritchessis, and for myn hond foond ful many thingis;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 if Y siy the sunne, whanne it schynede, and the moone goynge clereli;
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 and if myn herte was glad in priuyte, and if Y kisside myn hond with my mouth;
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 which is the moost wickidnesse, and deniyng ayens hiyeste God;
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 if Y hadde ioye at the fallyng of hym, that hatide me, and if Y ioide fulli, that yuel hadde founde hym;
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 for Y yaf not my throte to do synne, that Y schulde asaile and curse his soule;
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 if the men of my tabernacle seiden not, Who yyueth, that we be fillid of hise fleischis? a pilgryme dwellide not with outforth;
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 my dore was opyn to a weiegoere;
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 if Y as man hidde my synne, and helide my wickidnesse in my bosum;
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 if Y dredde at ful greet multitude, and if dispisyng of neyyboris made me aferd; and not more Y was stille, and yede not out of the dore;
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 who yyueth an helpere to me, that Almyyti God here my desire? that he that demeth,
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 write a book, that Y bere it in my schuldre, and cumpasse it as a coroun to me?
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Bi alle my degrees Y schal pronounce it, and Y schal as offre it to the prynce.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 If my lond crieth ayens me, and hise forewis wepen with it;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 if Y eet fruytis therof with out money, and Y turmentide the soule of erthetileris of it;
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 a brere growe to me for wheete, and a thorn for barli.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< Job 31 >