< Job 22 >

1 Forsothe Eliphat Themanytes answeride, and seide,
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Whether a man, yhe, whanne he is of perfit kunnyng, mai be comparisound to God?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 What profitith it to God, if thou art iust? ethir what schalt thou yyue to hym, if thi lijf is without wem?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Whether he schal drede, and schal repreue thee, and schal come with thee in to doom,
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 and not for thi ful myche malice, and thi wickidnessis with out noumbre, `these peynes bifelden iustli to thee?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 For thou hast take awei with out cause the wed of thi britheren; and hast spuylid nakid men of clothis.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Thou yauest not watir to the feynt man; and thou withdrowist breed fro the hungri man.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 In the strengthe of thin arm thou haddist the lond in possessioun; and thou moost myyti heldist it.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Thou leftist widewis voide; and al to-brakist the schuldris of fadirles children.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Therfor thou art cumpassid with snaris; and sodeyn drede disturblith thee.
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 And thou gessidist, that thou schuldist not se derknessis; and that thou schuldist not be oppressid with the fersnesse of watris flowyng.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Whether thou thenkist, that God is hiyere than heuene, and is enhaunsid aboue the coppe of sterris?
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 And thou seist, What sotheli knowith God? and, He demeth as bi derknesse.
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 A cloude is his hidyng place, and he biholdith not oure thingis, and he `goith aboute the herris of heuene.
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Whether thou coueitist to kepe the path of worldis, which wickid men han ofte go?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Whiche weren takun awei bifor her tyme, and the flood distriede the foundement of hem.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Whiche seiden to God, Go thou awei fro vs; and as if Almyyti God may do no thing, thei gessiden hym,
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 whanne he hadde fillid her housis with goodis; the sentence of whiche men be fer fro me.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 Iust men schulen se, and schulen be glad; and an innocent man schal scorne hem.
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 Whether the reisyng of hem is not kit doun, and fier schal deuoure the relifs of hem?
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Therfor assente thou to God, and haue thou pees; and bi these thingis thou schalt haue best fruytis.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Take thou the lawe of his mouth, and sette thou hise wordis in thin herte.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 If thou turnest ayen to Almyyti God, thou schalt be bildid; and thou schalt make wickidnesse fer fro thi tabernacle.
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 He schal yyue a flynt for erthe, and goldun strondis for a flynt.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 And Almyyti God schal be ayens thin enemyes; and siluer schal be gaderid togidere to thee.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Thanne on Almyyti God thou schalt flowe with delicis; and thou schalt reise thi face to God.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Thou schalt preye hym, and he schal here thee; and thou schalt yelde thi vowis.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Thou schalt deme a thing, and it schal come to thee; and lyyt schal schyne in thi weies.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 For he that is mekid, schal be in glorie; and he that bowith doun hise iyen, schal be saued.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 An innocent schal be saued; sotheli he schal be saued in the clennesse of hise hondis.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Job 22 >