< Job 19 >

1 Forsothe Joob answeride, and seide, Hou long turmente ye my soule,
Sai Ayuba ya amsa,
2 and al to-breken me with wordis?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Lo! ten sithis ye schenden me, and ye ben not aschamed, oppressynge me.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Forsothe and if Y `koude not, myn vnkynnyng schal be with me.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 And ye ben reisid ayens me, and repreuen me with my schenschipis.
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Nameli now vndurstonde ye, that God hath turmentid me not bi euene doom, and hath cumpassid me with hise betyngis.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Lo! Y suffrynge violence schal crye, and no man schal here; Y schal crye loude, and `noon is that demeth.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 He bisette aboute my path, and Y may not go; and he settide derknessis in my weie.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 He hath spuylid me of my glorye, and hath take awey the coroun fro myn heed.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He hath distried me on ech side, and Y perischide; and he hath take awei myn hope, as fro a tre pullid vp bi the roote.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 His stronge veniaunce was wrooth ayens me; and he hadde me so as his enemye.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 Hise theues camen togidere, and `maden to hem a wei bi me; and bisegiden my tabernacle in cumpas.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 He made fer my britheren fro me; and my knowun as aliens yeden awei fro me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My neiyboris forsoken me; and thei that knewen me han foryete me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 The tenauntis of myn hows, and myn handmaydis hadden me as a straunger; and Y was as a pilgrym bifor her iyen.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 Y clepide my seruaunt, and he answeride not to me; with myn owne mouth Y preiede hym.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 My wijf wlatide my breeth; and Y preiede the sones of my wombe.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Also foolis dispisiden me; and whanne Y was goon awei fro hem, thei bacbitiden me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 Thei, that weren my counselouris sum tyme, hadden abhomynacioun of me; and he, whom Y louede moost, was aduersarie to me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Whanne fleischis weren wastid, my boon cleuyde to my skyn; and `oneli lippis ben left aboute my teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Haue ye merci on me, haue ye merci on me, nameli, ye my frendis; for the hond of the Lord hath touchid me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Whi pursuen ye me, as God pursueth; and ben fillid with my fleischis?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Who yyueth to me, that my wordis be writun? Who yyueth to me,
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 that tho be writun in a book with an yrun poyntil, ethir with a plate of leed; ethir with a chisel be grauun in a flynt?
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 For Y woot, that myn ayenbiere lyueth, and in the laste dai Y schal rise fro the erthe;
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 and eft Y schal be cumpassid with my skyn, and in my fleisch Y schal se God, my sauyour.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Whom Y my silf schal se, and myn iyen schulen biholde, and not an other man. This myn hope is kept in my bosum.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Whi therfor seien ye now, Pursue we hym, and fynde we the roote of a word ayens hym?
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Therfor fle ye fro the face of the swerd; for the swerd is the vengere of wickidnessis, and wite ye, that doom schal be.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >