< Job 1 >

1 `A man, Joob bi name, was in the lond of Hus; and thilke man was symple, and riytful, and dredynge God, and goynge awey fro yuel.
A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
2 And seuene sones and thre douytris weren borun to hym;
Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
3 and his possessioun was seuene thousynde of scheep, and thre thousynde of camels, and fyue hundrid yockis of oxis, and fyue hundrid of femal assis, and ful myche meynee; and `thilke man was grete among alle men of the eest.
yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
4 And hise sones yeden, and maden feestis bi housis, ech man in his day; and thei senten, and clepiden her thre sistris, `that thei schulden ete, and drynke wiyn with hem.
’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
5 And whanne the daies of feeste hadden passid in to the world, Joob sente to hem, and halewide hem, and he roos eerli, and offride brent sacrifices `bi alle. For he seide, Lest perauenture my sones do synne, and curse God in her hertis. Joob dide so in alle daies.
Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
6 Forsothe in sum day, whanne the sones of God `weren comun to be present bifor the Lord, also Sathan cam among hem.
Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
7 To whom the Lord seide, Fro whennus comest thou? Which answeride, and seide, Y haue cumpassid the erthe, and Y haue walkid thorouy it.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
8 And the Lord seide to hym, Whether thou hast biholde my seruaunt Joob, that noon in erthe is lyik hym; he is a symple man, and riytful, and dredynge God, and goynge awei fro yuel?
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
9 To whom Sathan answeride, Whether Joob dredith God veynli?
Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
10 Whethir thou hast not cumpassid hym, and his hows, and al his catel bi cumpas? Thou hast blessid the werkis of hise hondis, and hise possessioun encreesside in erthe.
Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
11 But stretche forth thin hond a litil, and touche thou alle thingis whiche he hath in possessioun; if he cursith not thee `in the face, `bileue not to me.
Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
12 Therfor the Lord seide to Sathan, Lo! alle thingis, whiche he hath, ben in thin hond; oneli stretche thou not forth thin hond in to hym. And Sathan yede out fro the face of the Lord.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
13 Sotheli whanne in sum dai `hise sones and douytris eeten, and drunken wiyn in the hows of her firste gendrid brothir,
Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
14 a messanger cam to Job, `whiche messanger seide, Oxis eriden, and femal assis `weren lesewid bisidis tho;
sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
15 and Sabeis felden yn, and token awey alle thingis, and `smytiden the children with swerd; and Y aloone ascapide for to telle to thee.
sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
16 And whanne he spak yit, anothir cam, and seide, Fier of God cam doun fro heuene, and wastide scheep, and `children touchid; and Y aloone ascapide for to telle `to thee.
Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
17 But yit the while he spak, also anothir cam, and seide, Caldeis maden thre cumpenyes, and assailiden the camels, and token tho awei, and thei smytiden `also the children with swerd; and Y aloone ascapide to telle to thee.
Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
18 And yit he spak, and, lo! anothir entride, and seide, While thi sones and douytris eeten, and drunken wiyn in the hows of her firste gendrid brothir,
Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
19 a greet wynde felde yn sudenli fro the coost of desert, and schook foure corneris of the hows, `which felde doun, and oppresside thi children, and thei ben deed; and Y aloone fledde to telle to thee.
sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
20 Thanne Joob roos, and to-rente hise clothis, and `with pollid heed he felde doun on the erthe, and worschipide God,
Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
21 and seide, Y yede nakid out of the wombe of my modir, Y schal turne ayen nakid thidur; the Lord yaf, the Lord took awei; as it pleside the Lord, so `it is doon; the name of the Lord be blessid.
ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
22 In alle these thingis Joob synnede not in hise lippis, nether spak ony fonned thing ayens God.
Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.

< Job 1 >