< Jeremiah 9 >
1 Who schal yyue watir to myn heed, and a welle of teeris to myn iyen? And Y schal biwepe dai and niyt the slayn men of the douyter of my puple.
Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
2 Who schal yyue me in to a wildirnesse of dyuerse weigoeris? And I schal forsake my puple, and Y schal go awei fro hem. For whi alle ben auowteris, and the cumpenyes of trespassouris ayens the lawe;
Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
3 and thei helden forth her tunge as a bouwe of leesyng, and not of treuthe Thei ben coumfortid in erthe, for thei yeden out fro yuel to yuel, and thei knewen not me, seith the Lord.
“Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
4 Ech man kepe hym fro his neiybore, and haue no trist in ony brother of hym; for whi ech brother disseyuyng schal disseyue, and ech frend schal go gilefuli.
“Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
5 And a man schal scorne his brother, and schal not speke treuthe; for thei tauyten her tunge to speke leesyng; thei traueliden to do wickidli.
Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
6 Thi dwellyng is in the myddis of gile; in gile thei forsoken to knowe me, seith the Lord.
Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
7 Therfor the Lord of oostis seith these thingis, Lo! Y schal welle togidere, and Y schal preue hem; for whi what other thing schal Y do fro the face of the douyter of my puple?
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
8 The tunge of hem is an arowe woundynge, and spak gile; in his mouth he spekith pees with his frend, and priueli he settith tresouns to hym.
Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
9 Whether Y schal not visite on these thingis, seith the Lord, ether schal not my soule take veniaunce on siche a folc?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
10 On hillis Y schal take wepyng and mournyng, and weilyng on the faire thingis of desert, for tho ben brent; for no man is passynge forth, and thei herden not the vois of hym that weldith; fro a brid of the eir `til to scheep, tho passiden ouer, and yeden awei.
Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
11 And Y schal yyue Jerusalem in to heepis of grauel, and in to dennes of dragouns; and Y schal yyue the citees of Juda in to desolacioun, for ther is no dwellere.
“Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
12 Who is a wise man that schal vndurstonde these thingis, and to whom the word of the mouth of the Lord schal be maad, that he telle this? Whi the erthe perischide, it is brent as desert, for noon is that passith?
Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
13 And the Lord seide, For thei forsoken my lawe, which Y yaf to hem, and thei herden not my vois, and thei yeden not therynne;
Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
14 and thei yeden aftir the schrewidnesse of her herte, and aftir Baalym, which thei lerneden of her fadris;
A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
15 therfor the Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Lo! Y schal fede this puple with wermod, and Y schal yyue to hem drynke the watir of galle.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
16 And Y schal scatere hem among hethene men, whiche thei and her fadris knewen not; and Y schal sende swerd aftir hem, til thei ben wastid.
Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
17 The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Biholde ye, and clepe ye wymmen `that weilen, and come thei; and sende ye to tho wymmen that ben wise, and haste thei.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
18 Haste thei, and take thei weilynge on you; youre iyen brynge doun teeris, and youre iyelidis flowe with watris;
Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
19 for the vois of weilyng is herd fro Sion. Hou ben we distried, and schent greetli? for we han forsake the lond, for oure tabernaclis ben forsakun.
An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
20 Therfor, wymmen, here ye the word of the Lord, and youre eeris take the word of his mouth; and teche ye youre douytris weilyng, and ech womman teche hir neiybore mournyng.
Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
21 For whi deth stiede bi youre wyndows, it entride in to youre housis, to leese litle children with outforth, and yonge men fro the stretis.
Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
22 Speke thou, the Lord seith, these thingis, And the deed bodi of a man schal fal doun as a toord on the face of the cuntrei, and as hei bihynde the bak of the mowere, and noon is that gaderith.
Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
23 The Lord seith these thingis, A wise man haue not glorie in his wisdom, and a strong man haue not glorie in his strengthe, and a riche man haue not glorie in hise richessis; but he that hath glorie,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
24 haue glorie in this, to wite and knowe me, for Y am the Lord, that do merci and dom and riytfulnesse in erthe. For whi these thingis plesen me, seith the Lord.
amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
25 Lo! daies comen, seith the Lord, and Y schal visite on ech man that hath prepucie vncircumcidid; on Egipt,
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
26 and on Juda, and on Edom, and on the sones of Amon, and on Moab, and on alle men that ben clippid on long heer, and dwellen in desert; for whi alle hethene men han prepucie, forsothe al the hous of Israel ben vncircumcidid in herte.
Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”