< Jeremiah 6 >

1 Sones of Beniamyn, be ye coumfortid in the myddil of Jerusalem, and make ye noise with a clarioun in Thecua, and reise ye a baner on Bethecarem; for whi yuel and greet sorewe is seyn fro the north.
“Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
2 Y haue licned the douytir of Sion to a fair womman and delicat.
Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
3 Scheepherdis and her flockis schulen come to it; thei han piyt tentis in it in cumpas; ech man schal feede hem, that ben vndur his hond.
Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
4 Halewe ye batel on it. Rise ye togidire, and stie we in myddai. Wo to vs, for the dai is bowid doun, for shadewis ben maad lengere in the euentid.
“Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
5 Rise ye, and stie we in the niyt, and distry we the housis therof.
Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
6 For the Lord of oostis seith these thingis, Kitte ye doun the tre therof, and schede ye erthe aboute Jerusalem; this is the citee of visitacioun; al fals caleng is in the myddis therof.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
7 As a cisterne makith his water coold, so it made his malice coold; wickidnesse and distriyng schal euer be herd ther ynne bifore me, sikenesse and wounde.
Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
8 Jerusalem, be thou tauyt, lest perauenture my soule go awei fro thee; lest perauenture Y sette thee forsakun, a loond vnhabitable.
Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
9 The Lord of oostis seith these thingis, Thei schulen gadere til to a racyn, thei schulen gadere the remenauntis of Israel as in a vyner; turne thin hond, as a gaderer of grapis to the bascat.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
10 To whom schal Y speke, and to whom schal Y seie witnessing, that he here? Lo! the eeris of hem ben vncircumcidid, and thei moun not here; lo! the word of the Lord is maad to hem in to dispit, and thei schulen not resseiue it.
Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
11 Therfor Y am ful of the strong veniaunce of the Lord, and Y trauelide suffrynge. Schede thou out on a litil child with outforth, and on the counsel of yonge men togidere; for a man with his wijf schal be takun, and an eeld man with him that is ful of daies.
Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
12 And the housis of hem, the feeldis and wyues togidere, schulen go to othere men; for Y schal stretche forth myn hond on the dwelleris of the lond, seith the Lord.
Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
13 For fro the lesse `til to the grettere, alle studien to auerise; and alle doon gile, fro the profete `til to the preest.
“Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
14 And thei heeliden the sorewe of the douyter of my puple with yuel fame, seiynge, Pees, pees, and no pees was.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
15 Thei ben schent, that diden abhomynacioun; yhe, rathere thei weren not schent bi confusioun, and thei kouden not be aschamed. Wherfor thei schulen falle doun among hem that schulen falle doun; thei schulen falle doun in the tyme of her visitacioun, seith the Lord.
Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
16 The Lord seith these thingis, Stonde ye on weies, and se ye, and axe ye of elde pathis, which is the good weie; and go ye ther ynne, and ye schulen fynde refreischyng to youre soulis. And thei seiden, We schulen not go.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
17 And Y ordeynede aspieris on you, and Y seide, Here ye the vois of a trumpe. And thei seiden, We schulen not here.
Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
18 Therfor, hethene men, here ye, and, thou congregacioun, knowe, hou grete thingis Y schal do to hem.
Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
19 Thou erthe, here, lo! Y schal brynge yuels on this puple, the fruit of her thouytis; for thei herden not my wordis, and castiden awei my lawe.
Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
20 Wherto bryngen ye to me encense fro Saba, and a tre of spicerie smellynge swetli fro a fer lond? Youre brent sacrifices ben not acceptid, and youre slayn sacrifices plesiden not me.
Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
21 Therfor the Lord God seith these thingis, Lo! Y schal yyue fallyngis in to this puple, and fadris and sones togidere, a neiybore and kynesman, schulen falle in hem, and schulen perische.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
22 The Lord God seith these thingis, Lo! a puple cometh fro the lond of the north, and a greet folk schal rise togidere fro the endis of erthe.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
23 It schal take an arowe and scheld; it is cruel, and schal not haue merci; the vois therof schal sowne as the see, and thei maad redi as a man to batel schulen stie on horsis ayens thee, thou douyter of Sion.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
24 We herden the fame therof, oure hondis ben `a clumsid; tribulacioun hath take vs, sorewis han take vs as a womman trauelinge of child.
Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 Nyle ye go out to the feeldis, and go ye not in the weie, for the swerd of the enemye, drede in cumpas.
Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
26 The douytir of my puple, be thou gird with heire, and be thou spreynt togidere with aische; make to thee mourenyng of oon aloone gendrid sone, a bitter weilyng, for whi a wastere schal come sodenli on you.
Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
27 I yaf thee a strong preuere in my puple, and thou schalt knowe, and preue the weie of hem.
“Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
28 Alle these princis bowynge awei, goynge gilefuli, ben metal and irun; alle ben corrupt.
Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
29 The belu failide, leed is waastid in the fier, the wellere wellide in veyn; for the malices of hem ben not wastid.
Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
30 Clepe ye hem repreuable siluer, for the Lord hath cast hem awei.
Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”

< Jeremiah 6 >