< Jeremiah 39 >

1 In the nynethe yeer of Sedechie, kyng of Juda, in the tenthe monethe, Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, and al his oost cam to Jerusalem, and thei bisegiden it.
A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
2 Forsothe in the enleuenthe yeer of Sedechie, in the fourthe monethe, in the fyuethe day of the monethe, the citee was opened;
A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
3 and alle the princes of the kyng of Babiloyne entriden, and saten in the myddil yate, Veregel, Fererer, Semegar, Nabusarrachym, Rapsaces, Neregel, Sereser, Rebynag, and alle othere princes of the kyng of Babiloyne.
Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
4 And whanne Sedechie, the kyng of Juda, and alle the men werriouris hadden seien hem, thei fledden, and yeden out bi niyt fro the citee, bi the weie of the gardyn of the kyng, and bi the yate that was bitwixe twei wallis; and thei yeden out to the weie of desert.
Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
5 Forsothe the oost of Caldeis pursueden hem, and thei token Sedechie in the feeld of wildirnesse of Jericho; and thei token hym, and brouyten to Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, in Reblatha, which is in the lond of Emath; and Nabugodonosor spak domes to hym.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
6 And the kyng of Babiloyne killide the sones of Sedechye in Reblatha, bifor hise iyen; and the kyng of Babyloyne killide alle the noble men of Juda.
A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
7 Also he puttide out the iyen of Sedechie, and boond hym in feteris, that he schulde be led in to Babiloyne.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
8 And Caldeis brenten with fier the hous of the kyng, and the hous of the comun puple, and distrieden the wal of Jerusalem.
Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
9 And Nabusardan, the maister of knyytis, translatide in to Babiloyne the residues of the puple, that dwelliden in the citee, and the fleeris awei, that hadden fled ouer to hym, and the superflue men of the comyn puple, that weren left.
Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
10 And Nabusardan, the maistir of knyytis, lefte in the lond of Juda, of the puple of pore men, and yaf to hem vyneris and cisternes in that dai.
Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
11 Forsothe Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, hadde comaundid of Jeremye to Nabusardan, maister of chyualrie, and seide,
To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
12 Take thou him, and sette thin iyen on hym, and do thou no thing of yuel to him; but as he wole, so do thou to hym.
“Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
13 Therfor Nabusardan, the prynce of chyualrie, sente Nabu, and Lesban, and Rapsases, and Veregel, and Sereser, and Rebynag, and alle the principal men of the kyng of Babiloyne,
Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
14 senten, and token Jeremye fro the porche of the prisoun, and bitokun hym to Godolie, the sone of Aicham, sone of Saphan, that he schulde entre in to the hous, and dwelle among the puple.
suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
15 Forsothe the word of the Lord was maad to Jeremye, whanne he was closid in the porche of the prisoun, and seide,
Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
16 Go thou, and seie to Abdemelech Ethiopien, and speke thou, The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Lo! Y schal brynge my wordis on this citee in to yuel, and not in to good; and tho schulen be in thi siyt in that dai.
“Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
17 And Y schal delyuere thee in that day, seith the Lord, and thou schalt not be bitakun in to the hondis of men, whiche thou dreddist;
Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
18 but Y delyuerynge schal delyuere thee, and thou schalt not falle doun bi swerd; but thi soule schal be in to helthe to thee, for thou haddist trist in me, seith the Lord.
Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”

< Jeremiah 39 >