< Jeremiah 37 >

1 And kyng Sedechie, the sone of Josie, regnede for Jeconye, the sone of Joachym, whom Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, made kyng in the lond of Juda.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
2 And he, and hise seruauntis, and his puple obeieden not to the wordis of the Lord, whiche he spak in the hond of Jeremye, the profete.
Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
3 And kyng Sedechie sente Jothal, the sone of Selemye, and Sofonye, the preest, the sone of Maasie, to Jeremye, the profete, and seide, Preie thou for vs oure Lord God.
Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
4 Forsothe Jeremye yede freli in the myddis of the puple; for thei hadden not sente hym in to the kepyng of the prisoun.
To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
5 Therfor the oost of Farao yede out of Egipt, and Caldeis, that bisegiden Jerusalem, herden sich a message, and yeden awei fro Jerusalem.
Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
6 And the word of the Lord was maad to Jeremye, the profete,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
7 and seide, The Lord God of Israel seith these thingis, Thus ye schulen seie to the kyng of Juda, that sente you to axe me, Lo! the oost of Farao, which yede out to you in to help, schal turne ayen in to his lond, in to Egipt.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
8 And Caldeis schulen come ayen, and schulen fiyte ayens this citee, and schulen take it, and schulen brenne it bi fier.
Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
9 The Lord seith these thingis, Nyle ye disseyue youre soulis, seiynge, Caldeis goynge schulen go a wey, and schulen departe fro vs; for thei schulen not go a wei.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
10 But thouy ye sleen al the oost of Caldeis, that fiyten ayens you, and summe woundid men of hem be left, ech man schal rise fro his tente, and thei schulen brenne this citee bi fier.
Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
11 Therfor whanne the oost of Caldeis hadde goon awei fro Jerusalem, for the oost of Farao, Jeremye yede out of Jerusalem,
Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
12 to go in to the lond of Beniamyn, and to departe there the possessioun in the siyt of citeseyns.
sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
13 And whanne he was comun to the yate of Beniamyn, ther was a kepere of the yate bi whiles, Jerie bi name, the sone of Selemye, sone of Ananye; and he took Jeremye, the prophete, and seide, Thou fleest to Caldeis.
Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
14 And Jeremye answeride, It is fals; Y fle not to Caldeis. And he herde not Jeremye, but Jerie took Jeremye, and brouyte hym to the princes.
Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
15 Wherfor the princes weren wrooth ayens Jeremye, and beeten hym, and senten hym in to the prisoun, that was in the hous of Jonathas, the scryuen; for he was souereyn on the prisoun.
Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
16 Therfor Jeremye entride in to the hous of the lake, and in to the prisoun of trauel; and Jeremye sat there manye daies.
Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
17 Therfor kyng Sedechie sente, and took hym a wei, and axide hym priuyli in his hous, and seide, Gessist thou, whether a word is of the Lord? And Jeremye seide, Ther is. And Jeremye seide, Thou schalt be bitakun in to the hond of the kyng of Babiloyne.
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
18 And Jeremye seide to Sedechie, the kyng, What haue Y synned to thee, and to thi seruauntis, and to thi puple, for thou hast sent me in to the hous of prisoun?
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
19 Where ben youre profetis, that profesieden to you, and seiden, The king of Babiloyne schal not come on you, and on this lond?
Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
20 Now therfor, my lord the kyng, Y biseche, here thou, my preier be worth in thi siyt, and sende thou not me ayen in to the hous of Jonathas, the scryuen, lest Y die there.
Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
21 Therfor Sedechie comaundide, that Jeremye schulde be bitakun in to the porche of the prisoun, and that a cake of breed schulde be youun to hym ech dai, outakun seew, til alle looues of the citee weren wastid; and Jeremye dwellide in the porche of the prisoun.
Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.

< Jeremiah 37 >