< Jeremiah 18 >

1 The word that was maad of the Lord to Jeremye,
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2 and seide, Rise thou, and go doun in to the hous of a pottere, and there thou schalt here my wordis.
“Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
3 And Y yede doun in to the hous of a pottere, and lo! he made a werk on a wheel.
Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
4 And the vessel was distried, which he made of clei with hise hondis; and he turnede it, and made it another vessel, as it pleside in hise iyen to make.
Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
5 And the word of the Lord was maad to me,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
6 and he seide, Whether as this pottere doith, Y mai not do to you, the hous of Israel? seith the Lord. Lo! as cley is in the hond of a pottere, so ye, the hous of Israel, ben in myn hond.
“Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
7 Sudenli Y schal speke ayens a folk, and ayens a rewme, that Y drawe out, and distrie, and leese it.
A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
8 If thilke folk doith penaunce of his yuel, which Y spak ayens it, also Y schal do penaunce on the yuel, which Y thouyte to do to it.
in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
9 And Y schal speke sudenli of a folk, and of a rewme, that Y bilde, and plaunte it.
In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
10 If it doith yuel bifore myn iyen, that it here not my vois, Y schal do penaunce on the good which Y spak, that Y schulde do to it.
in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
11 Now therfor seie thou to a man of Juda, and to the dwellere of Jerusalem, and seie, The Lord seith these thingis, Lo! Y make yuel ayens you, and Y thenke a thouyte ayens you; ech man turne ayen fro his yuel weie, and dresse ye youre weies and youre studies.
“Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
12 Whiche seiden, We han dispeirid, for we schulen go after oure thouytis, and we schulen do ech man the schrewidnesse of his yuel herte.
Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
13 Therfor the Lord seith these thingis, Axe ye hethene men, who herde siche orible thingis, whiche the virgyn of Israel hath do greetli?
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
14 Whether snow of the Liban schal fail fro the stoon of the feeld? ether coolde watris brekynge out, and fletynge doun moun be takun awei?
Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
15 For my puple hath foryete me, and offriden sacrifices in veyn, and snaperiden in her weies, and in the pathis of the world, that thei yeden bi tho in a weie not trodun;
Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
16 that the lond of hem schulde be in to desolacioun, and in to an hissyng euerlastinge; for whi ech that passith bi it, schal be astonyed, and schal moue his heed.
Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
17 As a brennynge wynd Y schal scatere hem bifor the enemy; Y schal schewe to hem the bak and not the face, in the dai of the perdicioun of hem.
Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
18 And thei seiden, Come ye, and thenke we thouytis ayens Jeremye; for whi the lawe schal not perische fro a preest, nether councel schal perische fro a wijs man, nether word schal perische fro a profete; come ye, and smyte we hym with tunge, and take we noon heede to alle the wordis of hym.
Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
19 Lord, yyue thou tent to me, and here thou the vois of myn aduersaries.
Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
20 Whether yuel is yoldun for good, for thei han diggid a pit to my soule; haue thou mynde, that Y stoode in thi siyt, to speke good for hem, and to turne awei thin indignacioun fro hem.
Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
21 Therfor yyue thou the sones of hem in to hungur, and lede forth hem in to the hondis of swerd; the wyues of hem be maad with out children, and be maad widewis, and the hosebondis of hem be slayn bi deth; the yonge men of hem be persid togidere bi swerd in batel.
Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
22 Cry be herd of the housis of hem, for thou schalt bringe sudenli a theef on hem; for thei diggiden a pit to take me, and hidden snaris to my feet.
Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
23 But thou, Lord, knowist al the councel of hem ayens me in to deth; do thou not merci to the wickidnesse of hem, and the synne of hem be not doon awei fro thi face; be thei maad fallynge doun in thi siyt, in the tyme of thi stronge veniaunce; vse thou hem to othir thing than thei weren ordeyned.
Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.

< Jeremiah 18 >