< Jeremiah 15 >

1 And the Lord seide to me, Thouy Moises and Samuel stoden bifore me, my soule is not to this puple; caste thou hem out fro my face, and go thei out.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
2 That if thei seien to thee, Whidur schulen we go out? thou schalt seie to hem, The Lord seith these thingis, Thei that to deth, to deth, and thei that to swerd, to swerd, and thei that to hungur, to hungur, and thei that to caitiftee, to caitifte.
In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
3 Y schal visite on hem foure spices, seith the Lord; a swerd to sleeynge, and doggis for to reende, and volatilis of the eir, and beestis of the erthe to deuoure and to distrie.
“Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
4 And Y schal yyue hem in to feruour to alle rewmes of erthe, for Manasses, the sone of Ezechie, king of Juda, on alle thingis whiche he dide in Jerusalem.
Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
5 For whi who schal haue merci on thee, Jerusalem, ethir who schal be sori for thee, ether who schal go to preie for thi pees?
“Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
6 Thou hast forsake me, seith the Lord, thou hast go abac; and Y schal stretche forth myn hond on thee, and Y schal sle thee; Y trauelide preiyng.
Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
7 And Y schal scatere hem with a wyndewynge instrument in the yatis of erthe; Y killide, and loste my puple, and netheles thei turneden not ayen fro her weies.
Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
8 The widewis therof ben multiplied to me aboue the grauel of the see; and Y brouyte in to hem a distriere in myddai on the modir of a yonge man, Y sente drede sudeynli on citees.
Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
9 Sche was sijk that childide seuene, hir soule failide; the sunne yede doun to hir, whanne dai was yit. Sche was schent, and was aschamed; and Y schal yyue the residue therof in to swerd in the siyt of her enemyes, seith the Lord.
Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
10 Mi modir, wo to me; whi gendridist thou me a man of chidyng, a man of discord in al the lond? Y lente not, nether ony man lente to me; alle men cursen me, the Lord seith.
Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
11 No man bileue to me, if thi remenauntis be not in to good, if Y ranne not to thee in the tyme of turment, and in the tyme of tribulacioun and of anguysch, ayens the enemye.
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
12 Whether yrun and metal schal be ioyned bi pees to irun fro the north?
“Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
13 And Y schal yyue freli thi ritchessis and thi tresouris in to rauyschyng, for alle thi synnes, and in alle thin endis.
“Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
14 And Y schal brynge thin enemyes fro the lond which thou knowist not; for fier is kyndlid in my strong veniaunce, and it schal brenne on you.
Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
15 Lord, thou knowist, haue thou mynde on me, and visite me, and delyuere me fro hem that pursuen me; nyle thou take me in thi pacience, knowe thou, that Y suffride schenschipe for thee.
Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
16 Thi wordis ben foundun, and Y eet tho; and thi word was maad to me in to ioye, and in to gladnesse of myn herte; for thi name, Lord God of oostis, is clepid to help on me.
Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
17 Y sat not in the counsel of pleieris, and Y hadde glorie for the face of thin hond; Y sat aloone, for thou fillidist me with bittirnesse.
Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
18 Whi is my sorewe maad euerlastinge, and my wounde dispeirid forsook to be curid? it is maad to me, as a leesyng of vnfeithful watris.
Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
19 For this thing the Lord seith these thingis, If thou turnest, Y schal turne thee, and thou schalt stonde bifore my face; and if thou departist preciouse thing fro vijl thing, thou schalt be as my mouth; thei schulen be turned to thee, and thou schalt not be turned to hem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
20 And Y schal yyue thee in to a brasun wal and strong to this puple, and thei schulen fiyte ayens thee, and schulen not haue the victorie; for Y am with thee, to saue thee, and to delyuere thee, seith the Lord.
Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
21 And Y schal delyuere thee fro the hond of the worste men, and Y schal ayenbie thee fro the hond of stronge men.
“Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”

< Jeremiah 15 >