< Jeremiah 13 >

1 The Lord seith these thingis to me, Go, and take in possessioun to thee a lynnun breigirdil; and thou schalt putte it on thi leendis, and thou schalt not bere it in to watir.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2 And Y took in possessioun a breigirdil, bi the word of the Lord; and Y puttide aboute my leendis.
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3 And the word of the Lord was maad to me in the secounde tyme,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4 and seide, Take the brigirdil, which thou haddist in possessioun, which is aboute thi leendis; and rise thou, and go to Eufrates, and hide thou it there, in the hoole of a stoon.
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5 And Y yede, and hidde it in Eufrates, as the Lord comaundide to me.
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
6 And it was don aftir ful many daies, the Lord seide to me, Rise thou, and go to Eufrates, and take fro thennus the brigirdil, whiche Y comaundide to thee, that thou schuldist hide it there.
Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
7 And Y yede to Eufrates, and diggide out, and Y took the breigirdil fro the place, where Y hadde hidde it; and lo! the breigirdil was rotun, so that it was not able to ony vss.
Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
8 And the word of the Lord was maad to me,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 and seide, The Lord seith these thingis, So Y schal make rotun the pride of Juda, and the myche pride of Jerusalem,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
10 and this worste puple, that nylen here my wordis, and goen in the schrewidnesse of her herte; and thei yeden aftir alien goddis, to serue hem, and to worschipe hem; and thei schulen be as this breigirdil, which is not able to ony vss.
Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
11 For as a breigirdil cleueth to the leendis of a man, so Y ioynede faste to me al the hous of Israel, and al the hous of Juda, seith the Lord, that thei schulden be to me in to a puple, and in to name, and in to heriyng, and in to glorie; and thei herden not.
Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
12 Therfor thou schalt seie to hem this word, The Lord God of Israel seith these thingis, Ech potel schal be fillid of wyn. And thei schulen seie to thee, Whether we witen not, that ech potel schal be fillid of wyn?
“Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
13 And thou schalt seie to hem, The Lord seith these thingis, Lo! Y shal fille with drunkenesse alle the dwelleris of this lond, and the kyngis of the generacioun of Dauith, that sitten on his trone, and the prestis, and profetis, and alle the dwelleris of Jerusalem.
Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
14 And Y schal scatere hem, a man fro his brother, and the fadris and sones togidere, seith the Lord; Y schal not spare, and Y schal not graunte, nether Y schal do mercy, that I leese not hem.
Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
15 Here ye, and perseyue with eeris; nyle ye be reisid, for the Lord spak.
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16 Yyue ye glorie to youre Lord God, bifore that it wexe derk, and bifor that youre feet hirte at derk hillis; ye schulen abide liyt, and he schal sette it in to the schadewe of deeth, and in to derknesse.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
17 That if ye heren not this, my soule schal wepe in hid place for the face of pride; it wepynge schal wepe, and myn iye shal caste out a teer, for the floc of the Lord is takun.
Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
18 Seye thou to the kyng, and to the ladi, Be ye mekid, sitte ye, for the coroun of youre glorie schal go doun fro youre heed.
Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
19 The cities of the south ben closid, and noon is that openith; al Juda is translatid bi perfit passyng ouere, ether goynge out of her lond.
Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
20 Reise ye youre iyen, and se ye, what men comen fro the north; where is the floc which is youun to thee, thi noble scheep?
Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
21 What schalt thou seie, whanne he schal visite thee? for thou hast tauyt hem ayens thee, and thou hast tauyt ayens thin heed. Whether sorewis han not take thee, as a womman trauelynge of child?
Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
22 That if thou seist in thin herte, Whi camen these thingis to me? for the multitude of thi wickidnesse thi schamefulere thingis ben schewid, thi feet ben defoulid.
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23 If a man of Ethiopie mai chaunge his skyn, ether a pard mai chaunge hise dyuersitees, and ye moun do wel, whanne ye han lerned yuel.
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24 And Y schal sowe hem abrood, as stobil which is rauyschid of the wynd in desert.
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25 This is thi lot, and the part of thi mesure of me, seith the Lord; for thou foryetidist me, and tristidist in a leesyng.
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26 Wherfor and Y made nakid thin hipis ayens thi face, and thi schenschipe apperide,
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27 thin auowtries, and thin neyyng, and the felonye of thi fornycacioun on litle hillis in the feeld; Y siy thin abhomynaciouns. Jerusalem, wo to thee, thou schalt not be clensid after me til yit.
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”

< Jeremiah 13 >