< Isaiah 45 >
1 The Lord seith these thingis to my crist, Cirus, whos riythond Y took, that Y make suget folkis bifor his face, and turne the backis of kyngis; and Y schal opene yatis bifore hym, and yatis schulen not be closid.
“Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
2 Y schal go bifore thee, and Y schal make lowe the gloriouse men of erthe; Y schal al to-breke brasun yatis, and Y schal breke togidere irun barris.
Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
3 And Y schal yyue hid tresours to thee, and the priuy thingis of priuytees, that thou wite, that Y am the Lord, that clepe thi name, God of Israel,
Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
4 for my seruaunt Jacob, and Israel my chosun, and Y clepide thee bi thi name; Y licnyde thee, and thou knewist not me.
Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
5 Y am the Lord, and ther is no more; with out me is no God. Y haue gird thee, and thou knewist not me.
Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
6 That thei that ben at the risyng of the sunne, and thei that ben at the west, know, that with out me is no God.
saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
7 Y am the Lord, and noon other God is; fourmynge liyt, and makynge derknessis, makynge pees, and fourmynge yuel; Y am the Lord, doynge alle these thingis.
Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
8 Heuenes, sende ye out deew fro aboue, and cloudis, reyne a iust man; the erthe be openyde, and brynge forth the sauyour, and riytfulnesse be borun togidere; Y the Lord haue maad hym of nouyt.
“Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
9 Wo to hym that ayen seith his maker, a tiel stoon of erthe of Sannys. Whether clei seith to his pottere, What makist thou, and thi werk is withouten hondis?
“Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
10 Wo to hym that seith to the fadir, What gendrist thou? and to a womman, What childist thou?
Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
11 The Lord, the hooli of Israel, the fourmere therof, seith these thingis, Axe ye me thingis to comynge on my sones, and sende ye to me on the werkis of myn hondis.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
12 Y made erthe, and Y made a man on it; myn hondis helden abrood heuenes, and Y comaundide to al the knyythod of tho.
Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
13 Y reiside hym to riytfulnesse, and Y schal dresse alle hise weies; he schal bilde my citee, and he schal delyuere my prisoneris, not in prijs, nether in yiftis, seith the Lord of oostis.
Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
14 The Lord God seith these thingis, The trauel of Egipt, and the marchaundie of Ethiopie, and of Sabaym; hiy men schulen go to thee, and schulen be thine; thei schulen go aftir thee, thei schulen go boundun in manyclis, and schulen worschipe thee, and schulen biseche thee. God is oneli in thee, and with out thee is no God.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
15 Verili thou art God hid, God, the sauyour of Israel.
Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
16 Alle makeris of errours ben schent, and weren aschamed; thei yeden togidere in to confusioun.
Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
17 Israel is sauyde in the Lord, bi euerlastynge helthe; ye schulen not be schent, and ye schulen not be aschamed, til in to the world of world.
Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
18 For whi the Lord makynge heuenes of nouyt, seith these thingis; he is God fourmynge erthe, and makinge it, he is the makere therof; he made it of noyt, not in veyn, but he formyde it, that it be enhabitid; Y am the Lord, and noon other is.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
19 Y spak not in hid place, not in a derk place of erthe; I seide not to the seed of Jacob, Seke ye me in veyn. Y am the Lord spekynge riytfulnesse, tellynge riytful thingis.
Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
20 Be ye gaderid, and come ye, and neiye ye togidere, that ben sauyd of hethene men; thei that reisen a signe of her grauyng, knewen not, and thei preien a god that saueth not.
“Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
21 Telle ye, and come ye, and take ye councel togidere. Who made this herd fro the bigynnyng? fro that tyme Y bifor seide it. Whether Y am not the Lord, and no God is ferthere with out me? God riytful and sauynge is noon, outakun me.
Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
22 Alle the coostis of erthe, be ye conuertid to me, and ye schulen be saaf; for Y am the Lord, and noon other is.
“Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
23 Y swoor in my silf, a word of riytfulnesse schal go out of my mouth, and it schal not turne ayen; for ech kne schal be bowid to me, and ech tunge schal swere.
Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
24 Therfor thei schulen sei in the Lord, Riytfulnessis and empire ben myne; alle that fiyten ayens hym schulen come to hym, and schulen be aschamed.
Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
25 Al the seed of Israel schal be iustified and preysid in the Lord.
Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.