< Isaiah 29 >

1 Wo! Ariel, Ariel, the citee which Dauid ouercam; yeer is addid to yeer, solempnytees ben passyd.
Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
2 And Y schal cumpasse Ariel, and it schal be soreuful and morenynge; and Jerusalem schal be to me as Ariel.
Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
3 And Y schal cumpasse as a round trendil in thi cumpasse, and Y schal caste erthe ayens thee, and Y schal sette engynes in to thi bisegyng.
Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
4 Thou schalt be maad low, thou schalt speke of erthe, and thi speche schal be herd fro the erthe; and thi vois schal be as the vois of a deed man reisid bi coniuring, and thi speche schal ofte grutche of the erthe.
Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
5 And the multitude of hem that wyndewen thee, schal be as thynne dust; and the multitude of hem that hadden the maistrie ayens thee, schal be as a deed sparcle passynge.
Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
6 And it schal be sudenli, anoon it schal be visitid of the Lord of oostis, in thundur, and in mouyng of the erthe, and in greet vois of whirlwynd, and of tempest, and of flawme of fier deuowrynge.
Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
7 And the multitude of alle folkis that fouyten ayens Ariel schal be as the dreem of a nyytis visioun; and alle men that fouyten, and bisegiden, and hadden the maistrie ayens it.
Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
8 And as an hungry man dremyth, and etith, but whanne he is awakid, his soule is voide; and as a thirsti man dremeth, and drynkith, and after that he is awakid, he is weri, and thirstith yit, and his soule is voide, so schal be the multitude of alle folkis, that fouyten ayens the hil of Sion.
kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
9 Be ye astonyed, and wondre; wake ye, and douyte ye; be ye drunken, and not of wyn; be ye moued, and not with drunkenesse.
Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
10 For the Lord hath meddlid to you the spirit of sleep; he schal close youre iyen, and schal hile youre profetis, and princes that sien visiouns.
Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
11 And the visioun of alle profetis schal be to you as the wordis of a book aseelid; which whanne thei schulen yyue to hym that kan lettris, thei schulen seie, Rede thou this book; and he schal answere, Y may not, for it is aseelid.
Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
12 And the book schal be youun to him that kan not lettris, and it schal be seid to hym, Rede thou; and he schal answere, Y kan no lettris.
Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
13 And the Lord seide, For that this puple neiyeth with her mouth, and glorifieth me with her lippis, but her herte is fer fro me; and thei dredden me for the comaundement and techyngis of men, therfor lo!
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
14 Y schal adde, that Y make wondryng to this puple, in a greet myracle and wondurful; for whi wisdom schal perische fro wise men therof, and the vndurstondyng of prudent men therof schal be hid.
Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
15 Wo to you that ben hiye of herte, that ye hide counsel fro the Lord; the werkis of whiche ben in derknessis, and thei seien, Who seeth vs, and who knowith vs?
Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
16 This thouyt of you is weiward, as if cley thenke ayens a pottere, and the werk seie to his makere, Thou madist not me; and a thing `that is maad, seie to his makere, Thou vndurstondist not.
Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
17 Whether not yit in a litil time and schort the Liban schal be turned in to Chermel, and Chermel schal be arettid in to the forest?
Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
18 And in that dai deef men schulen here the wordis of the book, and the iyen of blynde men schulen se fro derknessis and myisty;
A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
19 and mylde men schulen encreesse gladnesse in the Lord, and pore men schulen make ful out ioie in the hooli of Israel.
Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
20 For he that hadde the maistrie, failide, and the scornere is endid, and alle thei ben kit doun that walkiden on wickidnesse;
Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
21 whiche maden men to do synne in word, and disseyueden a repreuere in the yate, and bowiden awey in veyn fro a iust man.
waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
22 For this thing the Lord, that ayen bouyte Abraham, seith these thingis to the hous of Jacob, Jacob schal not be confoundid now, nether now his cheer schal be aschamed; but whanne he schal se hise sones,
Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
23 the werkis of myn hondis, halewynge my name in the myddis of hym. And thei schulen halewe the hooli of Jacob, and thei schulen preche God of Israel;
Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
24 and thei that erren in spirit, schulen knowe vndurstondyng, and idil men schulen lerne the lawe.
Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”

< Isaiah 29 >