< Isaiah 12 >

1 And thou schalt seie in that dai, Lord, Y schal knouleche to thee, for thou were wrooth to me; thi strong venieaunce is turned, and thou hast coumfortid me.
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
2 Lo! God is my sauyour, Y schal do feithfuli, and Y schal not drede. For whi the Lord is my strengthe and my preysyng, and he is maad to me in to helthe.
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
3 Ye schulen drawe watris with ioie of the wellis of the sauyour.
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
4 And ye schulen seie in that dai, Knouleche ye to the Lord, and clepe ye his name in to help; make ye knowun hise fyndyngis among puplis; haue ye mynde, that his name is hiy.
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
5 Synge ye to the Lord, for he hath do worschipfuli; telle ye this in al erthe.
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
6 Thou dwellyng of Syon, make ful out ioie, and preise; for whi the hooli of Israel is greet in the myddis of thee.
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”

< Isaiah 12 >