< Hosea 13 >
1 For Effraym spak, hidousnesse assailide Israel; and he trespasside in Baal, and was deed.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 And now thei addiden to do synne, and maden to hem a yotun ymage of her siluer, as the licnesse of idols; al is the makyng of crafti men. To these thei seien, A! ye men, offre, and worschipe caluys.
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 Therfor thei schulen be as a morewtid cloude, and as the deew of morewtid, that passith forth, as dust rauyschide bi whirlewynd fro the corn floor, and as smoke of a chymenei.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 Forsothe Y am thi Lord God, `that ledde thee fro the loond of Egipt; and thou schalt not knowe God, outakun me, and no sauyour is, outakun me.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 Y knewe thee in the desert, in the lond of wildirnesse.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 Bi her lesewis thei weren fillid, and hadden abundaunce; thei reisiden her herte, and foryaten me.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 And Y schal be as a lionesse to hem, as a parde in the weye of Assiriens.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 Y as a femal bere, whanne the whelps ben rauyschid, schal mete hem; and schal al to-breke the ynnere thingis of the mawe of hem. And Y as a lioun schal waaste hem there; a beeste of the feeld schal al to-rende hem.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 Israel, thi perdicioun is of thee; thin help is oneli of me.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Where is thi kyng? moost saue he thee now in alle thi citees; and where ben thi iugis, of whiche thou seidist, Yyue thou to me a kyng, and princes?
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 Y schal yyue to thee a kyng in my strong veniaunce, and Y schal take awei in myn indignacioun.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 The wickidnesse of Effraym is boundun togidere; his synne is hid.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 The sorewis of a womman trauelynge of child schulen come to hym; he is a sone not wijs. For now he schal not stonde in the defoulyng of sones.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 Y schal delyuere hem fro the hoond of deeth, and Y schal ayenbie hem fro deth. Thou deth, Y schal be thi deth; thou helle, Y schal be thi mussel. (Sheol )
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
15 Coumfort is hid fro myn iyen, for he schal departe bitwixe britheren. The Lord schal brynge a brennynge wynd, stiynge fro desert; and it schal make drie the veynes therof, and it schal make desolat the welle therof; and he schal rauysche the tresour of ech desirable vessel.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Samarie perische, for it stiride his God to bittirnesse; perische it bi swerd. The litle children of hem be hurtlid doun, and the wymmen with child therof be koruun.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”