< Hosea 10 >
1 Israel was a vyne ful of bowis, fruyt was maad euene to hym; bi the multitude of his fruyt he multipliede auteris, bi the plente of his lond he was plenteuouse.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 In simylacris the herte of hem is departid, now thei schulen perische. He schal breke the simylacris of hem, he schal robbe the auteris of hem.
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 For thanne thei schulen seie, A kyng is not to vs, for we dreden not the Lord. And what schal a kyng do to vs?
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 Speke ye wordis of vnprofitable visioun, and ye schulen smyte boond of pees with leesyng; and doom as bittirnesse schal burioune on the forewis of the feeld.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 The dwelleris of Samarie worschipiden the kien of Bethauen. For the puple therof mourenyde on that calf, and the keperis of the hous therof; thei maden ful out ioye on it in the glorie therof, for it passide fro that puple.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 For also it was borun to Assur, a yifte to the king veniere. Confusioun schal take Effraym, and Israel schal be schent in his wille.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Samarie made his kyng to passe, as froth on the face of water. And the hiy thingis of idol, the synne of Israel, schulen be lost.
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 A cloote and a brere schal stie on the auters of hem. And thei schulen seie to mounteyns, Hile ye vs, and to litle hillis, Falle ye doun on vs.
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 Fro the daies of Gabaa Israel synnede; there thei stoden. Batel schal not take hem in Gabaa,
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 on the sones of wickidnesse. Bi my desir Y schal chastise hem; puplis schulen be gaderid togidere on hem, whanne thei schulen be chastisid for her twei wickidnessis.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Effraym is a cow calf, tauyt for to loue threischyng; and Y yede on the fairenesse of the necke therof. Y schal stie on Effraym. Judas schal ere, and Jacob schal breke forewis to hym silf.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Sowe ye to you riytfulnesse in treuthe, and repe ye in the mouthe of merci, and make ye newe to you a feld newli brouyte to tilthe. Forsothe tyme is to seke the Lord, whanne he cometh, that schal teche you riytfulnesse.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 Ye han erid vnfeithfulnesse, ye han rope wickidnesse, ye han ete the corn of leesyng. For thou tristydist in thi weles, and in the multitude of thi stronge men.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 Noise schal rise in thi puple, and alle thi stronge holdis schulen be distried; as Salmana was distried of the hous of hym, that took veniaunce on Baal; in the dai of batel, whanne the modir was hurlid doun on the sones.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 So Bethel dide to you, for the face of malice of youre wickidnessis.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.